Home Taska ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojojin Nijar 6

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojojin Nijar 6

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojojin Nijar 6

 

An kashe sojojin Nijar shida wani hari da ƴan bindiga suka kai kudu maso yammacin ƙasar, kusa da iyaka da Burkina Faso, kamar yadda ma’aikatar tsaron kasar ta sanar ranar Asabar.

Harin wanda aka kai a ranar Alhamis, shi ne na biyu cikin kwanaki 10 da ke nuna dawowar hare-hare a yankin bayan shafe makwanni ba a kai hari ba.

Sanarwar ma’aikatar tsaron ta ce “Wasu gungun ƴan ta’adda ɗauke da makamai sun yi wa ayarin sojojin Nijar kwanton ɓauna a kusa da kauyen Kolmane.”

Sanarwar ta ce sojoji shiga aka kashe yayin da ɗaya ya samu rauni da kuma mota da aka lalata. Babu ƙarin bayani kan makomar maharan.

Yankin Tallaberi ya sha fama da hare-hare musamman a yankunan da ke kan iyaka da Burkina Faso da Mali inda mayaƙa masu iƙirarin jihadi masu alaƙa da Al Qaeda da IS ke kai hare-hare.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp