Home Taska ‘Yan Sanda Sun Kama Wadanda Ake Zargi da Kashe ‘Yan Sanda Biyu...

‘Yan Sanda Sun Kama Wadanda Ake Zargi da Kashe ‘Yan Sanda Biyu a Anambra

Police-Arrest

Yan Sanda Sun Kama Wadanda Ake Zargi da Kashe ‘Yan Sanda Biyu a Anambra

 

An kama wasu ‘yan bindiga da ake zargin sun kai hari ofishin ‘yan sanda a jihar Anambra, inda suka kashe ‘yan sanda biyu.

Lamarin ya faru ne a karamar hukumar Okija da ke Ihiala a cikin watan Maris.

Kwamishinan ‘yan sandan kasar, Echeng Echeng ne ya sanar da kamen a jiya, inda ya ce an kama wanda ake zargin shi ne ya shirya harin tare da wasu mutanensa a ranar Laraba.

Echeng ya ce “An kama da yawa daga cikin wadanda ake kira ‘yan bindigar da ba a san ko su waye ba, an kwato makamai da motoci tare da ceto wadanda abin ya shafa.”

“A jiya (Laraba), mun samu ci gaba a rundunar. A watan Maris, an kai wa daya daga cikin tashoshinmu hari a Okija, kuma mun rasa mutanenmu biyu. Muna so mu sanar da ku cewa an kama wanda ya shirya wannan aiki ne a jiya tare da mutanensa uku.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp