‘Yan Sanda Sun Kama Wadanda Ake Zargi da Kashe ‘Yan Sanda Biyu a Anambra

Yan Sanda Sun Kama Wadanda Ake Zargi da Kashe ‘Yan Sanda Biyu a Anambra

 

An kama wasu ‘yan bindiga da ake zargin sun kai hari ofishin ‘yan sanda a jihar Anambra, inda suka kashe ‘yan sanda biyu.

Lamarin ya faru ne a karamar hukumar Okija da ke Ihiala a cikin watan Maris.

Kwamishinan ‘yan sandan kasar, Echeng Echeng ne ya sanar da kamen a jiya, inda ya ce an kama wanda ake zargin shi ne ya shirya harin tare da wasu mutanensa a ranar Laraba.

Echeng ya ce “An kama da yawa daga cikin wadanda ake kira ‘yan bindigar da ba a san ko su waye ba, an kwato makamai da motoci tare da ceto wadanda abin ya shafa.”

“A jiya (Laraba), mun samu ci gaba a rundunar. A watan Maris, an kai wa daya daga cikin tashoshinmu hari a Okija, kuma mun rasa mutanenmu biyu. Muna so mu sanar da ku cewa an kama wanda ya shirya wannan aiki ne a jiya tare da mutanensa uku.”

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 23 minutes 24 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 4 minutes 49 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com