Home Taska Kungiyar UKCCSG ta Nuna Rashin Jindadin ta Kan Yajin Aikin ‘Yan Adaidaita...

Kungiyar UKCCSG ta Nuna Rashin Jindadin ta Kan Yajin Aikin ‘Yan Adaidaita Sahu a Jahar Kano

Abike Dabiri CEO NIDCOM
Abike Dabiri CEO NIDCOM

Kungiyar UKCCSG ta Nuna Rashin Jindadin ta Kan Yajin Aikin ‘Yan Adaidaita Sahu a Jahar Kano

Inuwar kungiyoyi masu zaman kansu ta jihar kano, Mai labin Umbrella of kano concern civil Society groups, ta bukaci gwamnan jihar kano dr. Abdullahi Umar Ganduje daya sanya bakin cikin dambarawar dake faruwa tsakanin hukumar karota da matuka baburan Adaidaita sahu a jihar kano.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar Comrade Ibrahim Ali wadda aka raba manema labarai a yammacin Talata.

Sanarwa tace kungiyar ta lura da yadda al’ummar jihar kano suka shiga cikin mawuyacin hali sakamakon yajin aikin da kungiyoyin matuka baburan Adaidaita sahun suka tafi.

Yajin aiki da yayi sanadiyar dakatar da al’amaru da dama wanda ya hadar da dakatar da daliban makarantun sakandire, na Primary hadi da na kwalejoji da jami’oin jihar kano zuwa makarantun su.

Kungiyoyin suka ce matsayin su na kungiyoyin fararen hula, suna jajantawa Al’ummar jihar kano bisa wannan mataki da masu tuka baburan Adaidaita sahun suka dauka.

Sannan kuma suna kira ga gwamnan jihar jihar kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje daya sanya baki cikin wannan lamari, sannan yayi kira ga shugaban cin hukumar karota.

Kungiyar tace ta san gwamnatin jihar kano nada kyawawan manufofi, amma suna ganin kaar da gangan shugaban hukumar ta Karota ke yiwa gwamantin zagwan kasa ta hanyar furta kalamai masara dadi ga ‘ya’ayn kugiyar dake kukan hukumar na tsawwala musu wajen karabar haraji da sanya musu tara babu gaira babu dalili.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

Comments are closed.

Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp