Home Taska Kungiyar UKCCSG ta Nuna Rashin Jindadin ta Kan Yajin Aikin ‘Yan Adaidaita...

Kungiyar UKCCSG ta Nuna Rashin Jindadin ta Kan Yajin Aikin ‘Yan Adaidaita Sahu a Jahar Kano

Abike Dabiri CEO NIDCOM
Abike Dabiri CEO NIDCOM

Kungiyar UKCCSG ta Nuna Rashin Jindadin ta Kan Yajin Aikin ‘Yan Adaidaita Sahu a Jahar Kano

Inuwar kungiyoyi masu zaman kansu ta jihar kano, Mai labin Umbrella of kano concern civil Society groups, ta bukaci gwamnan jihar kano dr. Abdullahi Umar Ganduje daya sanya bakin cikin dambarawar dake faruwa tsakanin hukumar karota da matuka baburan Adaidaita sahu a jihar kano.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar Comrade Ibrahim Ali wadda aka raba manema labarai a yammacin Talata.

Sanarwa tace kungiyar ta lura da yadda al’ummar jihar kano suka shiga cikin mawuyacin hali sakamakon yajin aikin da kungiyoyin matuka baburan Adaidaita sahun suka tafi.

Yajin aiki da yayi sanadiyar dakatar da al’amaru da dama wanda ya hadar da dakatar da daliban makarantun sakandire, na Primary hadi da na kwalejoji da jami’oin jihar kano zuwa makarantun su.

Kungiyoyin suka ce matsayin su na kungiyoyin fararen hula, suna jajantawa Al’ummar jihar kano bisa wannan mataki da masu tuka baburan Adaidaita sahun suka dauka.

Sannan kuma suna kira ga gwamnan jihar jihar kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje daya sanya baki cikin wannan lamari, sannan yayi kira ga shugaban cin hukumar karota.

Kungiyar tace ta san gwamnatin jihar kano nada kyawawan manufofi, amma suna ganin kaar da gangan shugaban hukumar ta Karota ke yiwa gwamantin zagwan kasa ta hanyar furta kalamai masara dadi ga ‘ya’ayn kugiyar dake kukan hukumar na tsawwala musu wajen karabar haraji da sanya musu tara babu gaira babu dalili.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

Comments are closed.

Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp