Home Taska Kungiyar UKCCSG ta Nuna Rashin Jindadin ta Kan Yajin Aikin ‘Yan Adaidaita...

Kungiyar UKCCSG ta Nuna Rashin Jindadin ta Kan Yajin Aikin ‘Yan Adaidaita Sahu a Jahar Kano

Abike Dabiri CEO NIDCOM
Abike Dabiri CEO NIDCOM

Kungiyar UKCCSG ta Nuna Rashin Jindadin ta Kan Yajin Aikin ‘Yan Adaidaita Sahu a Jahar Kano

Inuwar kungiyoyi masu zaman kansu ta jihar kano, Mai labin Umbrella of kano concern civil Society groups, ta bukaci gwamnan jihar kano dr. Abdullahi Umar Ganduje daya sanya bakin cikin dambarawar dake faruwa tsakanin hukumar karota da matuka baburan Adaidaita sahu a jihar kano.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar Comrade Ibrahim Ali wadda aka raba manema labarai a yammacin Talata.

Sanarwa tace kungiyar ta lura da yadda al’ummar jihar kano suka shiga cikin mawuyacin hali sakamakon yajin aikin da kungiyoyin matuka baburan Adaidaita sahun suka tafi.

Yajin aiki da yayi sanadiyar dakatar da al’amaru da dama wanda ya hadar da dakatar da daliban makarantun sakandire, na Primary hadi da na kwalejoji da jami’oin jihar kano zuwa makarantun su.

Kungiyoyin suka ce matsayin su na kungiyoyin fararen hula, suna jajantawa Al’ummar jihar kano bisa wannan mataki da masu tuka baburan Adaidaita sahun suka dauka.

Sannan kuma suna kira ga gwamnan jihar jihar kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje daya sanya baki cikin wannan lamari, sannan yayi kira ga shugaban cin hukumar karota.

Kungiyar tace ta san gwamnatin jihar kano nada kyawawan manufofi, amma suna ganin kaar da gangan shugaban hukumar ta Karota ke yiwa gwamantin zagwan kasa ta hanyar furta kalamai masara dadi ga ‘ya’ayn kugiyar dake kukan hukumar na tsawwala musu wajen karabar haraji da sanya musu tara babu gaira babu dalili.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

Comments are closed.

Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp