Home Taska Hukumar NITDA ta Raba Kayan Aiki da Jari ga Matasa 140 Wadanda...

Hukumar NITDA ta Raba Kayan Aiki da Jari ga Matasa 140 Wadanda ta ba wa Horo Kan Gyaran Waya a Jihar Jigawa

Defence Minister Mansur Dan Ali Receives Souveniur from Italian Defence Minister Sen Roberta Pinnoti
Defence Minister Mansur Dan Ali Receives Souveniur from Italian Defence Minister Sen Roberta Pinnoti

Hukumar NITDA ta Raba Kayan Aiki da Jari ga Matasa 140 Wadanda ta ba wa Horo Kan Gyaran Waya a Jihar Jigawa

Hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), ƙarƙashin jagorancin Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), ta yaye matasa jimillar mutum (140) a Jihar Jigawa waɗanda ta ba wa horo kan sana’ar gyaran wayar salula a zamance gami da sauran harkokin fasaha, kana kuma ta raba musu jari haɗi da kayan aikin gudanar sana’ar domin dogaro da kai.

Horon na tsawon yini huɗu wanda aka gudanar da shi a ranar 31 ga watan Janairu, zuwa 4 ga watan Fabarairu, 2022 a cibiyoyi gudan biyu da aka ware a cikin garuruwan Dutse da Haɗejia, kowacce cibiya ta ɗauki jimilla mutane saba’in.

Kayan aikin sun haɗa da manyan wayoyi na hannu (Tablet), da sufanun sincewa da ɗaure waya, gami da kuɗin sufuri da sauransu. An kuma ilimantar da matasan salo da dabarun warware natsalolin wayar hannu a zamance.

Ko da a can baya, hukumar ta (NITDA) bisa kulawar ma’aikatar sadarwa da tattalin arziƙin fasahar zamani, ƙarƙashin jagorancin Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, (FNCS, FBCS, FIIM), ta ƙaddamar da irin wannan shiri a wasu daga cikin Jihohin ƙasar nan kamar Jihar Yobe. Manufar shirin ita ce fatan ganin matasa sun samu abin yi tattalin arziƙin ƙasa ya bunƙasa.

Litinin, 14 ga watan Fabarairu, 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp