Home Taska Hukumar NITDA ta Raba Kayan Aiki da Jari ga Matasa 140 Wadanda...

Hukumar NITDA ta Raba Kayan Aiki da Jari ga Matasa 140 Wadanda ta ba wa Horo Kan Gyaran Waya a Jihar Jigawa

Defence Minister Mansur Dan Ali Receives Souveniur from Italian Defence Minister Sen Roberta Pinnoti
Defence Minister Mansur Dan Ali Receives Souveniur from Italian Defence Minister Sen Roberta Pinnoti

Hukumar NITDA ta Raba Kayan Aiki da Jari ga Matasa 140 Wadanda ta ba wa Horo Kan Gyaran Waya a Jihar Jigawa

Hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), ƙarƙashin jagorancin Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), ta yaye matasa jimillar mutum (140) a Jihar Jigawa waɗanda ta ba wa horo kan sana’ar gyaran wayar salula a zamance gami da sauran harkokin fasaha, kana kuma ta raba musu jari haɗi da kayan aikin gudanar sana’ar domin dogaro da kai.

Horon na tsawon yini huɗu wanda aka gudanar da shi a ranar 31 ga watan Janairu, zuwa 4 ga watan Fabarairu, 2022 a cibiyoyi gudan biyu da aka ware a cikin garuruwan Dutse da Haɗejia, kowacce cibiya ta ɗauki jimilla mutane saba’in.

Kayan aikin sun haɗa da manyan wayoyi na hannu (Tablet), da sufanun sincewa da ɗaure waya, gami da kuɗin sufuri da sauransu. An kuma ilimantar da matasan salo da dabarun warware natsalolin wayar hannu a zamance.

Ko da a can baya, hukumar ta (NITDA) bisa kulawar ma’aikatar sadarwa da tattalin arziƙin fasahar zamani, ƙarƙashin jagorancin Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, (FNCS, FBCS, FIIM), ta ƙaddamar da irin wannan shiri a wasu daga cikin Jihohin ƙasar nan kamar Jihar Yobe. Manufar shirin ita ce fatan ganin matasa sun samu abin yi tattalin arziƙin ƙasa ya bunƙasa.

Litinin, 14 ga watan Fabarairu, 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp