Home Taska Hukumar NITDA ta Fara ba da Horo ga Mutane 200 Ƴan Gudun...

Hukumar NITDA ta Fara ba da Horo ga Mutane 200 Ƴan Gudun Hijira a Abuja

Hukumar NITDA ta Fara ba da Horo ga Mutane 200 Ƴan Gudun Hijira a Abuja

A ƙoƙarinta na cimma fata da burin mai girma shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, (GCFR), na fidda ƴan Nageriya kimanin mutum miliyan ɗari daga cikin ƙangin fatara gami da talauci, hukukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), ƙarƙashin jagorancin Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), ta ƙaddamar da shirinta na ba da horon ƙwarewa kan fasahar zamani ga ƴan gudun hijira, matafiya, da kuma waɗanda fitintinu su ka raba su da muhallansu.

Horon wanda za a shafe tsawon yini (5) ana gudanar da shi, an ƙaddamar da fara shi ne a yau a cibiyar horar da ma’aikata ilimin aikin gwamnati a zamanance, (E-Government Training Center), da ke yankin Kubuwa, birnin tarayya Abuja, kana haɗin gwiwa ne a tsakanin hukumar ta (NITDA) da kuma hukumar kula da al’amuran ƴan gudun hijira ta tarayyar Nageriya, “National Commission For Refugees Migrants And Internally Displaced Persons (NCFRMI).

Horon da ke da manufar bunƙasa ƙwarewa kan hikimomi da dabarun ilimin fasahar sadarwar zamani domin harkar kasuwanci da sana’o’in dogaro da kai a zamanance, kimanin mutane ɗari biyu ƴan gudun hijira, da masu ƙaura, da waɗanda iftila’i ya raba da muhallansu ne za su amfana a birnin Abuja kafin daga bisani kuma a faɗaɗa shirin zuwa sauran Jihohin Nageriya.

Mai girma shugaban ƙasa Malam Muhammadu Buhari, (GCFR), tuntuni ya yi alƙawarin fidda ƴan Nageriya kimanin mutum (Miliyan 100) daga cikin talauci nan da shekarar (2030) da yardar Allah. Wanda a ƙarƙashin wannan turba hukumar ta (NITDA), da ma’aikatar sadarwa, ƙarƙashin jagorancin Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, (FNCS, FBCS, FIIM), su ka himmatu ka’in da na’in wajen ba wa al’ummar Nageriya daban-daban horo kan hikimomi da dabaru na ilimin fasahar sadarwar zamani domin su samu sana’o’i da kasuwancin dogaro da kai.

Litinin, 14 ga watan Fabarairu, 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp