Home WASANNI Arsenal da Newcastle na Zawarcin ‘Dan Wasan AC Milan da Portugal Rafael...

Arsenal da Newcastle na Zawarcin ‘Dan Wasan AC Milan da Portugal Rafael Leao

Arsenal da Newcastle na Zawarcin ‘Dan Wasan AC Milan da Portugal Rafael Leao

Arsenal na tunanin zawarcin dan wasan gaban Chelsea Armando Broja, mai shekara 20. A halin yanzu dan wasan na Albania yana zaman aro ne a Southampton. (Football in London)

Chelsea ta ba da fifiko kan sayen dan wasan bayan Sevilla da Faransa Jules Kounde, mai shekara 23, a bazara, yayin da Blues kuma ke son dauko dan wasan tsakiya na West Ham da Ingila Declan Rice, mai shekara 23, da kuma dan wasan tsakiyar Monaco mai shekara 22 Aurelien Tchouameni. (Telegraph)

Kocin Leicester Brendan Rodgers ya ce dole ne su yi tunani game da makomar dan wasan tsakiyar Belgium Youri Tielemans, mai shekara 24, wanda ya shiga watanni 18 na karshen kwantiraginsa, a dai-dai lokacin da Arsenal da Manchester United ke sha’awarsa (Metro).

Kofar Juventus a bude take, don sayen dan wasan tsakiya na Faransa Adrien Rabiot, mai shekara 26, da dan wasan baya na Brazil Alex Sandro, mai shekara 31. (Gazzetta dello Sport).

Barcelona na fatan ganin ta dakile zawarcin dan wasan tsakiyar Spain Gavi, mai shekara 17, da dan wasan bayan Uruguay Ronald Araujo, ta hanyar sabunta kwantiragin ‘yan wasan biyu. Liverpool da Manchester United duk suna zawarcin Araujo mai shekaru 22. (ESPN)

Arsenal da Newcastle na zawarcin dan wasan AC Milan da Portugal Rafael Leao, mai shekara 22 a bazara. (Fichajes)

Pep Guardiola yana son Raheem Sterling, mai shekara 27, ya rattaba hannu kan sabon kwantaragi a Manchester City amma ya ce kungiyar za ta yanke shawara ta karshe kan makomar dan wasan na Ingila. Yarjejeniyar Sterling za ta kare ne a watan Yunin 2023 kuma ya ce a shirye yake ya koma wata kasar don ci gaba da buga wasanni (Independent)

Mauricio Pochettino na tunanin barin Paris St-Germain a bazarar nan bayan da ya samu sabani da manyan jiga-jigan kungiyar. (Goal)

Manchester United na sha’awar sayen dan wasan bayan Borussia Monchengladbach Ramy Bensebaini, mai shekara 26, kuma suna kallon dan wasan na Algeria a matsayin wanda zai maye gurbin dan wasan bayan Ingila na hagu Luke Shaw. (Fichajes)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp