Home WASANNI Arsenal da Newcastle na Zawarcin ‘Dan Wasan AC Milan da Portugal Rafael...

Arsenal da Newcastle na Zawarcin ‘Dan Wasan AC Milan da Portugal Rafael Leao

Arsenal da Newcastle na Zawarcin ‘Dan Wasan AC Milan da Portugal Rafael Leao

Arsenal na tunanin zawarcin dan wasan gaban Chelsea Armando Broja, mai shekara 20. A halin yanzu dan wasan na Albania yana zaman aro ne a Southampton. (Football in London)

Chelsea ta ba da fifiko kan sayen dan wasan bayan Sevilla da Faransa Jules Kounde, mai shekara 23, a bazara, yayin da Blues kuma ke son dauko dan wasan tsakiya na West Ham da Ingila Declan Rice, mai shekara 23, da kuma dan wasan tsakiyar Monaco mai shekara 22 Aurelien Tchouameni. (Telegraph)

Kocin Leicester Brendan Rodgers ya ce dole ne su yi tunani game da makomar dan wasan tsakiyar Belgium Youri Tielemans, mai shekara 24, wanda ya shiga watanni 18 na karshen kwantiraginsa, a dai-dai lokacin da Arsenal da Manchester United ke sha’awarsa (Metro).

Kofar Juventus a bude take, don sayen dan wasan tsakiya na Faransa Adrien Rabiot, mai shekara 26, da dan wasan baya na Brazil Alex Sandro, mai shekara 31. (Gazzetta dello Sport).

Barcelona na fatan ganin ta dakile zawarcin dan wasan tsakiyar Spain Gavi, mai shekara 17, da dan wasan bayan Uruguay Ronald Araujo, ta hanyar sabunta kwantiragin ‘yan wasan biyu. Liverpool da Manchester United duk suna zawarcin Araujo mai shekaru 22. (ESPN)

Arsenal da Newcastle na zawarcin dan wasan AC Milan da Portugal Rafael Leao, mai shekara 22 a bazara. (Fichajes)

Pep Guardiola yana son Raheem Sterling, mai shekara 27, ya rattaba hannu kan sabon kwantaragi a Manchester City amma ya ce kungiyar za ta yanke shawara ta karshe kan makomar dan wasan na Ingila. Yarjejeniyar Sterling za ta kare ne a watan Yunin 2023 kuma ya ce a shirye yake ya koma wata kasar don ci gaba da buga wasanni (Independent)

Mauricio Pochettino na tunanin barin Paris St-Germain a bazarar nan bayan da ya samu sabani da manyan jiga-jigan kungiyar. (Goal)

Manchester United na sha’awar sayen dan wasan bayan Borussia Monchengladbach Ramy Bensebaini, mai shekara 26, kuma suna kallon dan wasan na Algeria a matsayin wanda zai maye gurbin dan wasan bayan Ingila na hagu Luke Shaw. (Fichajes)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp