Home WASANNI Arsenal da Newcastle na Zawarcin ‘Dan Wasan AC Milan da Portugal Rafael...

Arsenal da Newcastle na Zawarcin ‘Dan Wasan AC Milan da Portugal Rafael Leao

Arsenal da Newcastle na Zawarcin ‘Dan Wasan AC Milan da Portugal Rafael Leao

Arsenal na tunanin zawarcin dan wasan gaban Chelsea Armando Broja, mai shekara 20. A halin yanzu dan wasan na Albania yana zaman aro ne a Southampton. (Football in London)

Chelsea ta ba da fifiko kan sayen dan wasan bayan Sevilla da Faransa Jules Kounde, mai shekara 23, a bazara, yayin da Blues kuma ke son dauko dan wasan tsakiya na West Ham da Ingila Declan Rice, mai shekara 23, da kuma dan wasan tsakiyar Monaco mai shekara 22 Aurelien Tchouameni. (Telegraph)

Kocin Leicester Brendan Rodgers ya ce dole ne su yi tunani game da makomar dan wasan tsakiyar Belgium Youri Tielemans, mai shekara 24, wanda ya shiga watanni 18 na karshen kwantiraginsa, a dai-dai lokacin da Arsenal da Manchester United ke sha’awarsa (Metro).

Kofar Juventus a bude take, don sayen dan wasan tsakiya na Faransa Adrien Rabiot, mai shekara 26, da dan wasan baya na Brazil Alex Sandro, mai shekara 31. (Gazzetta dello Sport).

Barcelona na fatan ganin ta dakile zawarcin dan wasan tsakiyar Spain Gavi, mai shekara 17, da dan wasan bayan Uruguay Ronald Araujo, ta hanyar sabunta kwantiragin ‘yan wasan biyu. Liverpool da Manchester United duk suna zawarcin Araujo mai shekaru 22. (ESPN)

Arsenal da Newcastle na zawarcin dan wasan AC Milan da Portugal Rafael Leao, mai shekara 22 a bazara. (Fichajes)

Pep Guardiola yana son Raheem Sterling, mai shekara 27, ya rattaba hannu kan sabon kwantaragi a Manchester City amma ya ce kungiyar za ta yanke shawara ta karshe kan makomar dan wasan na Ingila. Yarjejeniyar Sterling za ta kare ne a watan Yunin 2023 kuma ya ce a shirye yake ya koma wata kasar don ci gaba da buga wasanni (Independent)

Mauricio Pochettino na tunanin barin Paris St-Germain a bazarar nan bayan da ya samu sabani da manyan jiga-jigan kungiyar. (Goal)

Manchester United na sha’awar sayen dan wasan bayan Borussia Monchengladbach Ramy Bensebaini, mai shekara 26, kuma suna kallon dan wasan na Algeria a matsayin wanda zai maye gurbin dan wasan bayan Ingila na hagu Luke Shaw. (Fichajes)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp