Home WASANNI Kano Pillars ta gabatar da sabbin ‘Yan wasa 12

Kano Pillars ta gabatar da sabbin ‘Yan wasa 12

Tawagar Kano Pillars FC, wacce ta lashe gasar Nigeria Premier Football League, NPFL, sau hudu, ta sanar da sababbin ‘yan wasan da ta dauka a hukumance gabanin kakar wasanni ta 2024/25.

An gudanar da taron bikin gabatar da sabbin ‘yan wasan a filin wasa na Sani Abacha a ranar Laraba, 4 ga Satumba, 2024, tare da halartar Shugaban tawagar, Alhaji Ali Muhammad Na Yara Mai Samba, gami da wasu daga cikin mambobin kwamitin gudanarwa.

A shirye-shiryen da take yi don sabuwar kakar wasannin, tawagar ta dauki sabbin ‘yan wasa guda goma sha biyu, tare da mai da hankali kan wasu muhimman wurare don kara karfin tawagar.

Wannan shiri ya nuna kudirin Kano Pillars FC na dawo da matsayinta na babbar tawagar ƙwallon kafar Nijeriya.

Sabbin ‘yan wasan sun hada da masu tsaron gida guda uku, wasu masu tsaron baya, ‘yan wasan tsakiya, da ‘yan wasan gaba, wadanda suka hada da ‘yan wasan cikin gida da kuma na kasashen waje.

Bugu da kari baya da sababbin ‘yan wasan da aka dauka, tawagar ta ci gaba da rike ‘yan wasa ashirin daga kakar wasannin da ta gabata, wanda hakan zai haifar da taka leda mai kyau ga tawagar.

Kano Pillars FC za ta fara buga gasar NPFL ta 2024/25 a ranar 8 ga Satumba, 2024, inda za ta rika buga wasanninta na gida a filin wasa na Muhammad Dikko da ke Katsina a matsayin wucin gadi, saboda gyare-gyaren da ake yi a filin wasa na Sani Abacha.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp