Home WASANNI Kano Pillars ta gabatar da sabbin ‘Yan wasa 12

Kano Pillars ta gabatar da sabbin ‘Yan wasa 12

Tawagar Kano Pillars FC, wacce ta lashe gasar Nigeria Premier Football League, NPFL, sau hudu, ta sanar da sababbin ‘yan wasan da ta dauka a hukumance gabanin kakar wasanni ta 2024/25.

An gudanar da taron bikin gabatar da sabbin ‘yan wasan a filin wasa na Sani Abacha a ranar Laraba, 4 ga Satumba, 2024, tare da halartar Shugaban tawagar, Alhaji Ali Muhammad Na Yara Mai Samba, gami da wasu daga cikin mambobin kwamitin gudanarwa.

A shirye-shiryen da take yi don sabuwar kakar wasannin, tawagar ta dauki sabbin ‘yan wasa guda goma sha biyu, tare da mai da hankali kan wasu muhimman wurare don kara karfin tawagar.

Wannan shiri ya nuna kudirin Kano Pillars FC na dawo da matsayinta na babbar tawagar ƙwallon kafar Nijeriya.

Sabbin ‘yan wasan sun hada da masu tsaron gida guda uku, wasu masu tsaron baya, ‘yan wasan tsakiya, da ‘yan wasan gaba, wadanda suka hada da ‘yan wasan cikin gida da kuma na kasashen waje.

Bugu da kari baya da sababbin ‘yan wasan da aka dauka, tawagar ta ci gaba da rike ‘yan wasa ashirin daga kakar wasannin da ta gabata, wanda hakan zai haifar da taka leda mai kyau ga tawagar.

Kano Pillars FC za ta fara buga gasar NPFL ta 2024/25 a ranar 8 ga Satumba, 2024, inda za ta rika buga wasanninta na gida a filin wasa na Muhammad Dikko da ke Katsina a matsayin wucin gadi, saboda gyare-gyaren da ake yi a filin wasa na Sani Abacha.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp