Home General Majalisar jihar Kano ta Amince da kudirin kara kasafin kudin jihar

Majalisar jihar Kano ta Amince da kudirin kara kasafin kudin jihar

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Majalisar dokokin jihar Kano ta amince da kudirin kara kasafin kudin jihar da naira biliyan 99.2

Kudirin ya samu karbuwa daga dukkan kwamitin majalisar baki daya bayan kammala karatu na uku a zauren majalisar a ranar Alhamis.

Gwamna Abba Yusuf ya gabatar da kudirin dokar ne a ranar 26 ga Agusta, 2024 inda ya nemi a kara kasafin kudin zuwa Naira biliyan 536, 559, 816, 357.84 maimakon Naira biliyan 437, 338, 312, 787 da aka sanya wa hannu a watan Disamba 2023.

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala zaman majalisar, shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar, Hon. Aminu Sa’ad, ya bayyana cewa, kashi 58 cikin 100 na kasafin kudin an ware su ne domin manyan ayyuka na more rayuwa yayin da kashi 42 cikin 100 kuma aka ware domin gudanar da ayyukan yau da kullum.

Hon. Sa’ad ya kara da cewa, karin kasafin kudin an yi shi ne domin aiwatar da zabukan kananan hukumomi da ke tafe, biyan sabon mafi karancin albashi, kudaden gudanarwa ga sabbin ma’aikatun da aka kafa da sake bude cibiyoyin koyar da sana’o’i da sauran ayyukan da gwamnati ta sa gaba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp