Home General Majalisar jihar Kano ta Amince da kudirin kara kasafin kudin jihar

Majalisar jihar Kano ta Amince da kudirin kara kasafin kudin jihar

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Majalisar dokokin jihar Kano ta amince da kudirin kara kasafin kudin jihar da naira biliyan 99.2

Kudirin ya samu karbuwa daga dukkan kwamitin majalisar baki daya bayan kammala karatu na uku a zauren majalisar a ranar Alhamis.

Gwamna Abba Yusuf ya gabatar da kudirin dokar ne a ranar 26 ga Agusta, 2024 inda ya nemi a kara kasafin kudin zuwa Naira biliyan 536, 559, 816, 357.84 maimakon Naira biliyan 437, 338, 312, 787 da aka sanya wa hannu a watan Disamba 2023.

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala zaman majalisar, shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar, Hon. Aminu Sa’ad, ya bayyana cewa, kashi 58 cikin 100 na kasafin kudin an ware su ne domin manyan ayyuka na more rayuwa yayin da kashi 42 cikin 100 kuma aka ware domin gudanar da ayyukan yau da kullum.

Hon. Sa’ad ya kara da cewa, karin kasafin kudin an yi shi ne domin aiwatar da zabukan kananan hukumomi da ke tafe, biyan sabon mafi karancin albashi, kudaden gudanarwa ga sabbin ma’aikatun da aka kafa da sake bude cibiyoyin koyar da sana’o’i da sauran ayyukan da gwamnati ta sa gaba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp