Home General Gwamnatin Nijeriya ta bar Jakki tana Tukan Taiki – Atiku

Gwamnatin Nijeriya ta bar Jakki tana Tukan Taiki – Atiku

Atiku

Tsohon mataimakain shugaban kasa kuma Jagoran adawar Najeriya, Atiku Abubakar, ya zargi gwamnatin ƙasar da mayar da hankali kan wasu abubuwa da ya kira marasa muhimmanci tare da yin watsi da matsala tsaro da ƙasar ke fama da ita.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, tsohon ɗan takarar shugaba ƙasar na jam’iyyar PDP ya yi Allah wadai da harin da mayaƙan Boko Haram suka kai jihar Yobe, da ya yi sanadin mutuwar mutane da dama.

Ya kuma yi tsokaci kan yawan tashe-tashen hankula da ke ci gaba da faruwa a jihohin Katsina da Sokoto da sauran sassan Arewa.

Atiku ya zargi gwamnati da cewa ta fi damuwa da kama masu zanga-zanga, maimakon magance matsalar rashin tsaro.

“Duk da mummunan zubar da jini da aka yi a Yobe, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama, da kuma ɓarnar da aka yi a ƙauyuka da dama a Katsina da Sakoto, da sauran garuruwan da ke yankin arewa maso yamma da arewa ta tsakiya, da dukkan alamu gwamnati ta fi mayar da hankali kan ayyukanta da sauran abubuwa da ba zu da muhimmanci.” in ji Atiku.

Atiku ya kuma yi nuni da tashe-tashen hankulan da ‘yan Boko Haram ke haifarwa da rigingimun siyasa a kudu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp