Home General Kotu ta dakatar KANSIEC karbar kudin form din takara a jihar Kano

Kotu ta dakatar KANSIEC karbar kudin form din takara a jihar Kano

Wata babbar kotun tarayya dake zamanta a birnin Abuja ta dakatar da hukumar zaben jihar Kano (KANSIEC) karbar kudin sayen form na naira miliyan goma da miliyan biyar ga ‘yan takarkarun dake zawarcin kujerun shugabancin kananan hukumomi da mazabu a jihar a zaben kananan hukumomin dake tafe na wucin gadi.

Da yake bayar da umarnin mai shari’a Emeka Nwite a ranar laraba, bisa karara da jam’iyyun Action Peoples Party (APP), Action Democratic Party (ADP), da Social Democratic Party (SDP), suka shigar da hukumar zaben jihar ta KANSIEC gaban kotun.

Idan dai za’a iya tunawa hukumar zaben ta saka kudin sayen naira miliyan 10 ga dukkan dan takarar dake da muradin tsayawa takarar shugabancin karamar hukuma, haka kuma naira miliyan biyar ga dukkan wanda ke zawarcin kujera a mazaba wato kansila.

Haka kuma hukumar ta sake yin mi’ara koma baya kan ranar zaben da ta sanya tun da fari na 26 ga watan Oktoba, in ta dawo da ita ba zuwa 30 ga watan Nuwamba shekarar 2024.

A Nijeriya dai ana kallon gwamnonin jihohin kasar na tururuwar gudanar da zaben kananan hukumomi ne bisa umarnin kotun kolin kasar na tabbatarwa da kananan hukumomin cin gashin kai.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp