Home General Kotu ta dakatar KANSIEC karbar kudin form din takara a jihar Kano

Kotu ta dakatar KANSIEC karbar kudin form din takara a jihar Kano

Wata babbar kotun tarayya dake zamanta a birnin Abuja ta dakatar da hukumar zaben jihar Kano (KANSIEC) karbar kudin sayen form na naira miliyan goma da miliyan biyar ga ‘yan takarkarun dake zawarcin kujerun shugabancin kananan hukumomi da mazabu a jihar a zaben kananan hukumomin dake tafe na wucin gadi.

Da yake bayar da umarnin mai shari’a Emeka Nwite a ranar laraba, bisa karara da jam’iyyun Action Peoples Party (APP), Action Democratic Party (ADP), da Social Democratic Party (SDP), suka shigar da hukumar zaben jihar ta KANSIEC gaban kotun.

Idan dai za’a iya tunawa hukumar zaben ta saka kudin sayen naira miliyan 10 ga dukkan dan takarar dake da muradin tsayawa takarar shugabancin karamar hukuma, haka kuma naira miliyan biyar ga dukkan wanda ke zawarcin kujera a mazaba wato kansila.

Haka kuma hukumar ta sake yin mi’ara koma baya kan ranar zaben da ta sanya tun da fari na 26 ga watan Oktoba, in ta dawo da ita ba zuwa 30 ga watan Nuwamba shekarar 2024.

A Nijeriya dai ana kallon gwamnonin jihohin kasar na tururuwar gudanar da zaben kananan hukumomi ne bisa umarnin kotun kolin kasar na tabbatarwa da kananan hukumomin cin gashin kai.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp