Home General Kotu ta dakatar KANSIEC karbar kudin form din takara a jihar Kano

Kotu ta dakatar KANSIEC karbar kudin form din takara a jihar Kano

Wata babbar kotun tarayya dake zamanta a birnin Abuja ta dakatar da hukumar zaben jihar Kano (KANSIEC) karbar kudin sayen form na naira miliyan goma da miliyan biyar ga ‘yan takarkarun dake zawarcin kujerun shugabancin kananan hukumomi da mazabu a jihar a zaben kananan hukumomin dake tafe na wucin gadi.

Da yake bayar da umarnin mai shari’a Emeka Nwite a ranar laraba, bisa karara da jam’iyyun Action Peoples Party (APP), Action Democratic Party (ADP), da Social Democratic Party (SDP), suka shigar da hukumar zaben jihar ta KANSIEC gaban kotun.

Idan dai za’a iya tunawa hukumar zaben ta saka kudin sayen naira miliyan 10 ga dukkan dan takarar dake da muradin tsayawa takarar shugabancin karamar hukuma, haka kuma naira miliyan biyar ga dukkan wanda ke zawarcin kujera a mazaba wato kansila.

Haka kuma hukumar ta sake yin mi’ara koma baya kan ranar zaben da ta sanya tun da fari na 26 ga watan Oktoba, in ta dawo da ita ba zuwa 30 ga watan Nuwamba shekarar 2024.

A Nijeriya dai ana kallon gwamnonin jihohin kasar na tururuwar gudanar da zaben kananan hukumomi ne bisa umarnin kotun kolin kasar na tabbatarwa da kananan hukumomin cin gashin kai.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp