Home General Kotu ta dakatar KANSIEC karbar kudin form din takara a jihar Kano

Kotu ta dakatar KANSIEC karbar kudin form din takara a jihar Kano

Wata babbar kotun tarayya dake zamanta a birnin Abuja ta dakatar da hukumar zaben jihar Kano (KANSIEC) karbar kudin sayen form na naira miliyan goma da miliyan biyar ga ‘yan takarkarun dake zawarcin kujerun shugabancin kananan hukumomi da mazabu a jihar a zaben kananan hukumomin dake tafe na wucin gadi.

Da yake bayar da umarnin mai shari’a Emeka Nwite a ranar laraba, bisa karara da jam’iyyun Action Peoples Party (APP), Action Democratic Party (ADP), da Social Democratic Party (SDP), suka shigar da hukumar zaben jihar ta KANSIEC gaban kotun.

Idan dai za’a iya tunawa hukumar zaben ta saka kudin sayen naira miliyan 10 ga dukkan dan takarar dake da muradin tsayawa takarar shugabancin karamar hukuma, haka kuma naira miliyan biyar ga dukkan wanda ke zawarcin kujera a mazaba wato kansila.

Haka kuma hukumar ta sake yin mi’ara koma baya kan ranar zaben da ta sanya tun da fari na 26 ga watan Oktoba, in ta dawo da ita ba zuwa 30 ga watan Nuwamba shekarar 2024.

A Nijeriya dai ana kallon gwamnonin jihohin kasar na tururuwar gudanar da zaben kananan hukumomi ne bisa umarnin kotun kolin kasar na tabbatarwa da kananan hukumomin cin gashin kai.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp