Home General Hukumar gidajen yarin Kano ta musanta zargin rashin bai wa fursunoni wadataccen...

Hukumar gidajen yarin Kano ta musanta zargin rashin bai wa fursunoni wadataccen abinci

Hukumar Kula da Gidajen Yarin Najeriya reshen jihar Kano ta musanta rahotonnin da wasu kafofin yaɗa labaran ƙasar suka ruwaito na rashin bai wa fursunonin da ke ɗaure a gidajen yarin jihar wadataccen abinci.

A baya-baya nan dai an yi ta samun labaran ƙorafe-ƙorafe kan rashin bai wa fursunonin wadataccen abinci a jihar a shafukan sada zumunta.

To sai dai cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar kula da gidajen yarin jihar, Musbahu Lawan K/Nasarawa ya fitar ya ce an yaɗa rahotonni ne kawai domin ɓata wa hukumarsu suna.

”Waɗannan rahotonni abin takaici ne, kuma hukumarmu na shaida wa al’umma cewa walwala da jin daɗin fusunoninmu shi ne babban abin da hukumarmu ta sanya a gaba, don haka ne koyaushe hukumarmu ke tabbatar wannan muradi duk kuwa da halin matsin tattalin arziki da ƙarsamu ke ciki”, in ji sanarwar.

Ya kuma ƙara da cewa ba abinci kawai hukumar hukumar ke bai wa fursunonin ba, har ma da ilimantar da su da kuma ba su horon sana’o’in dogaro da kai da za su taimaki rayuwarsu bayan kammala zaman gidan yarin.

A Najeriya ana yawan samun ƙorafe-ƙorafe kan halin da ɗaurarru ke ciki a gidajen yarin ƙasar, kama daga kula da lafiyarsu da abinci da kuma babbar matsalar cunkoson fursunoni a gidajen yarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp