Home WASANNI NPFL: Kungiyar Kano Pillars zata Dawo Buga Wasa Jihar Kano

NPFL: Kungiyar Kano Pillars zata Dawo Buga Wasa Jihar Kano

Hukumar kula da gasar firimiya ta Najeriya, Nigeria Professional Football League (NPFL), ta bai wa ƙungiyar ƙwallon kafa ta Kano Pillars damar ci gaba da buga wasanni a filin wasa na Sani Abacha da ke jihar Kano.

Wannan dai na cikin Wata sanarwa da hukumar ta aike wa kungiyar ta kano Pillars, inda  ta ce yanzu haka kungiyar nada damar buga wasannin a filin bayan duba na tsanaki da hukumar tayi.

Ta cikin sanarwar Hukumar ta ce wajibi ne kungiyar ta kano Pillars ta tanadi wani filin wasan da za ta ci gaba da buga wasanni da zarar an fara aikin gyara ciyawar filin taka leda ta filin kafin kammala shi.

Tuni kungiyar kwallon kafar ta kano Pillars ta amince da sharaɗin, har, inda tace za ta buga wasanta na gaba tare da kungiyar kwallon kafa ta Katsina United a Kano ranar 16 ga watan Afrilu.

Idan dai za’a iya tunawa kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ba ta buga wasa a gida ba a kakar bana sakamakon matakin da hukumar ta NPFL ta ɗauka, inda ta umarci a sauya ciyawar filin taka ledar.

Yanzu haka dai kungiyar ta Pillars na mataki na 13 da maki 26 bayan buga wasa 22 a kakar bana ta 2022/2023.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp