Home Taska An Samu Matar da ta Warke Daga Cutar Kanjamau a Amurka

An Samu Matar da ta Warke Daga Cutar Kanjamau a Amurka

An Samu Matar da ta Warke Daga Cutar Kanjamau a Amurka

Gamayyar wasu masana kimiyya sun samar da hanyar magance cutar kanjamau a kasar Amurka a yanzu.

Rahoton da kafafen yada labarai na waje suka fitar ya bayyana cewa, an samu matar da ta warke sarai daga kanjamau.

Sai dai, a wasu lokuta a 2009 da 2019 an samu wasu mutanen da suka warke daga cutar, ta wata hanyar daban.

Kasar Amurka – Wata mata da ake kira da ‘Majinyaciyar New York’ domin sakaya sunanta, an ba da rahoton cewa ta zama mace ta farko da ta warke sarai daga cutar kanjamau, TheCable ta tattaro.

An ce an sanar da wannan ci gaban ne a ranar Talata 15 ga watan Fabrairu a wani taro kan cututtuka mai taken: ‘Conference on Retroviruses and Opportunistic Infections’, wanda aka gudanar ta yanar gizo.

A cewar kafar labarai ta NBC, majinyaciyar ta sami magani ne a Cibiyar Kiwon Lafiya ta New York-Presbyterian Weill Cornell a kasar Amurka.

An ce ta kamu da cutar kanjamau a 2013, yayin da aka tabbatar da cewa tana dauke da cutar sankarar bargo a 2017.

Ya lamarin yake?

Hadin maganin, wanda aka ce ya kunshi amfani da jinin da aka dauko daga igiyar cibiya, ya mai da hankali ne ga inganta garkuwar jiki.

Hakazalika, rahoton ya ce, an yi amfani da tsarin jinya na haplo-cord transplant, wanda aka samar don fadada damar samar da maganin ciwon daji ga mutanen da ke da cutar jini.

A cewar jaridar New York Times, duk da cewa masu bincike sun ce suna ci gaba da sanya ido kan yadda ake samun murmurewa daga cutar, amma a cikin watanni 14 da suka gabata ba a gano matar tana dauke da cutar kanjamau ba.

Jinyar ta ya zama mai mahimmanci idan aka yi la’akari da cewa mata sun fi yawa daga cikin mutanen da ke dauke da cutar kanjamau a duniya.

Bisa kididdigar da hadin gwiwar shirin Majalisar Dinkin Duniya kan cutar kanjamau (UNAIDS) ta fitar a 2021, “kashi 53 na dukkan mutanen da ke dauke da cutar kanjamau mata ne da yara mata”.

A baya, kafin wannan sabon ci gaba, an ce wasu maza biyu sun warke sarai daga cutar kanjamau a 2009 da 2019, ta hanyar yi musu dashen bargo.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp