Home Taska Mogadishu: Mayaƙan Al-Shabab Sun Kai Hare-Hare Babban Birnin Somalia

Mogadishu: Mayaƙan Al-Shabab Sun Kai Hare-Hare Babban Birnin Somalia

Mogadishu: Mayaƙan Al-Shabab Sun Kai Hare-Hare Babban Birnin Somalia

Hukumomi a Somalia sun ce da sanyin safiyar yau Laraba mayakan Al-Shabab sun kai hari wani ofishin ‘yan sanda da wurin binciken ababen hawa a Mogadishu babban birnin ƙasar.

Tun tsakar dare ake jin karar harbe-harbe babu kakkautawa a wasu sassan birnin.

Ministan tsaron cikin gida Abdullahi Nor ya wallafa a shafin sada zumunta cewa jami’an tsaro sun yi nasarar murƙushe masu tayar da ƙayar bayan masu alaƙa da kungiyar Al-Qaeda.

Babu rahoton wanda ya jikkata ko asarar rai. A makon da ya wuce mutum shida ne suka mutu lokacin da wani dan kunar-bakin-wake ya ta da bam din da ke jikinsa.

Maharin ya yi nufin tayar da bam ɗin a wata karamar mota da ke dauke da wakilan gwamnati a wurin da ake yin zaben ‘yan majalisu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp