Home Taska Mogadishu: Mayaƙan Al-Shabab Sun Kai Hare-Hare Babban Birnin Somalia

Mogadishu: Mayaƙan Al-Shabab Sun Kai Hare-Hare Babban Birnin Somalia

Mogadishu: Mayaƙan Al-Shabab Sun Kai Hare-Hare Babban Birnin Somalia

Hukumomi a Somalia sun ce da sanyin safiyar yau Laraba mayakan Al-Shabab sun kai hari wani ofishin ‘yan sanda da wurin binciken ababen hawa a Mogadishu babban birnin ƙasar.

Tun tsakar dare ake jin karar harbe-harbe babu kakkautawa a wasu sassan birnin.

Ministan tsaron cikin gida Abdullahi Nor ya wallafa a shafin sada zumunta cewa jami’an tsaro sun yi nasarar murƙushe masu tayar da ƙayar bayan masu alaƙa da kungiyar Al-Qaeda.

Babu rahoton wanda ya jikkata ko asarar rai. A makon da ya wuce mutum shida ne suka mutu lokacin da wani dan kunar-bakin-wake ya ta da bam din da ke jikinsa.

Maharin ya yi nufin tayar da bam ɗin a wata karamar mota da ke dauke da wakilan gwamnati a wurin da ake yin zaben ‘yan majalisu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Obi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban JosMatsalar Tsaro:  An Kashe Manoma 6 a Jihar Kaduna An Zargi Kwankwaso da Sayen Fom ɗin Takara na Kujeru 69 a Jam'iyyar PRPƘasurgumin ɗan bindiga, Turji ya ɗauki Alhakin Kashe Sojoji a Jihar Sokoto
X whatsapp