Home Taska Mogadishu: Mayaƙan Al-Shabab Sun Kai Hare-Hare Babban Birnin Somalia

Mogadishu: Mayaƙan Al-Shabab Sun Kai Hare-Hare Babban Birnin Somalia

Mogadishu: Mayaƙan Al-Shabab Sun Kai Hare-Hare Babban Birnin Somalia

Hukumomi a Somalia sun ce da sanyin safiyar yau Laraba mayakan Al-Shabab sun kai hari wani ofishin ‘yan sanda da wurin binciken ababen hawa a Mogadishu babban birnin ƙasar.

Tun tsakar dare ake jin karar harbe-harbe babu kakkautawa a wasu sassan birnin.

Ministan tsaron cikin gida Abdullahi Nor ya wallafa a shafin sada zumunta cewa jami’an tsaro sun yi nasarar murƙushe masu tayar da ƙayar bayan masu alaƙa da kungiyar Al-Qaeda.

Babu rahoton wanda ya jikkata ko asarar rai. A makon da ya wuce mutum shida ne suka mutu lokacin da wani dan kunar-bakin-wake ya ta da bam din da ke jikinsa.

Maharin ya yi nufin tayar da bam ɗin a wata karamar mota da ke dauke da wakilan gwamnati a wurin da ake yin zaben ‘yan majalisu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp