Home Taska Minista Sadiya Umar Farouq ta Jajantawa Waɗanda Gobarar Sansanin ‘Yan Gudun Hijira...

Minista Sadiya Umar Farouq ta Jajantawa Waɗanda Gobarar Sansanin ‘Yan Gudun Hijira ta Shafa a Borno

Minista Sadiya Umar Farouq ta Jajantawa Waɗanda Gobarar Sansanin ‘Yan Gudun Hijira ta Shafa a Borno

 

Ministan Ma’aikatar kula da Al’amuran jin kai da sarrafa annoba da ci gaban al’umma, Ta jajantawa waɗanda gobarar ta shafa.

Maigirma Ministar ma’aikatar Al’amuran jin kai da sarrafa annoba da ci gaban Al’umma, Sadiya Umar Farouq, ta bayyana bakin cikinta kan asarar rayuka da dukiyoyi da aka yi a sansanin ‘yan gudun hijira na Muna El-Badawy, da ke Maiduguri a Jihar Borno.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da babban sakataren ma’aikatar, Bashir Nura Alkali ya fitar.

Ministar ta jajantawa iyalan waɗanda suka rasa ‘yan uwansu a gobarar.

A bayanin nata ministar ta kara da cewa, “Rahotannin da suka iso gare ni sun tabbatar da asarar rayuka, an kuma samu lalacewar matsugunai dubu uku (3,000).

Don haka Ministar tace, yawaitar barkewar gobara a Sansanonin ‘Yan gudun hijirar abin damuwa ne kuma Gwamnatin Tarayya da Hukumomin da abin ya shafa a Jihohin za su dauki matakan dakile afkuwar lamarin nan gaba.

A halin da ake ciki, Ministar tace “Na umurci Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta kasa da ta gaggauta aika kayan agaji ga wadanda abin ya shafa a sansanin, yayin da za a gudanar da tantance musabbabin gobarar da ma irin barnar da ta yi.

” Mai girma ministar tayi kira ga mutanen da ke zaune a sansanin ‘yan gudun hijiran da su yi taka-tsan-tsan don hana afkuwar barkewar gobara.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp