Home Taska Minista Sadiya Umar Farouq ta Jajantawa Waɗanda Gobarar Sansanin ‘Yan Gudun Hijira...

Minista Sadiya Umar Farouq ta Jajantawa Waɗanda Gobarar Sansanin ‘Yan Gudun Hijira ta Shafa a Borno

Minista Sadiya Umar Farouq ta Jajantawa Waɗanda Gobarar Sansanin ‘Yan Gudun Hijira ta Shafa a Borno

 

Ministan Ma’aikatar kula da Al’amuran jin kai da sarrafa annoba da ci gaban al’umma, Ta jajantawa waɗanda gobarar ta shafa.

Maigirma Ministar ma’aikatar Al’amuran jin kai da sarrafa annoba da ci gaban Al’umma, Sadiya Umar Farouq, ta bayyana bakin cikinta kan asarar rayuka da dukiyoyi da aka yi a sansanin ‘yan gudun hijira na Muna El-Badawy, da ke Maiduguri a Jihar Borno.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da babban sakataren ma’aikatar, Bashir Nura Alkali ya fitar.

Ministar ta jajantawa iyalan waɗanda suka rasa ‘yan uwansu a gobarar.

A bayanin nata ministar ta kara da cewa, “Rahotannin da suka iso gare ni sun tabbatar da asarar rayuka, an kuma samu lalacewar matsugunai dubu uku (3,000).

Don haka Ministar tace, yawaitar barkewar gobara a Sansanonin ‘Yan gudun hijirar abin damuwa ne kuma Gwamnatin Tarayya da Hukumomin da abin ya shafa a Jihohin za su dauki matakan dakile afkuwar lamarin nan gaba.

A halin da ake ciki, Ministar tace “Na umurci Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta kasa da ta gaggauta aika kayan agaji ga wadanda abin ya shafa a sansanin, yayin da za a gudanar da tantance musabbabin gobarar da ma irin barnar da ta yi.

” Mai girma ministar tayi kira ga mutanen da ke zaune a sansanin ‘yan gudun hijiran da su yi taka-tsan-tsan don hana afkuwar barkewar gobara.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp