Home SIYASA Kotu ta Bayar da Umarnin Kwace Kadarorin Tsohon Gwamnan Zamfara Abdulaziz Yari

Kotu ta Bayar da Umarnin Kwace Kadarorin Tsohon Gwamnan Zamfara Abdulaziz Yari

Kotu ta Bayar da Umarnin Kwace Kadarorin Tsohon Gwamnan Zamfara Abdulaziz Yari

 

Hukumar ICPC mai binciken laifukan cin hanci da rashawa a Najeriya ta ce wata Babbar Kotun Tarayya a Abuja ta ba ta umarni na wucin gadi na kwace wasu kadarorin tsohon Gwamnan Jahar Zamfara Abdulaziz Yari.

Kaddarorin sun haɗa da gine-gine da kudaden da tsohon gwamnan ya ajiye a wasu bankunan kasar.

A yau Laraba alkalan kotun karkashin jagorancin Mai Shari’a Obiora Egwuatu ta bayar da umarnin kwace kadarorin, ciki har da wasu gine-gine 10 da ke ciki da wajen Najeriya.

Kakakin hukumar Misis Azuka Ogugua ta tabbatar wa BBC Hausa cewa wannan nasarar ta wucin gadi ce, kuma bayan lokacin da kotun ta diba, gwamnatin Najeriya na iya kwace kadarorin idan tsohon gwamnan ya kasa gamsar da kotu cewa ya mallaki su ta halaliyar hanya.

Ta ce: “Abin da wannan ke nufi shi ne bayan lokacin da kotun ta diba, kuma babu wanda ya iya gamsar da shari’a cewa ya mallaki kadarorin ta halattacciyar hanya, kotu za ta mika wa gwamnatin tarayya dukkan kadarorin na dindindin ke nan.”

Wannan hukuncin na zuwa ne bayan wani hukunci irinsa da wata babbar kotun ta yanke tana bayar da umarnin a kwace kusan naira miliyan 279 ciki har da dalolin Amurka da ta gano tsohon gwamnan ya mallaka ta haramtacciyar hanya.

Wasu cikin kadarorin da aka kwace suna manyan unguwanni a biranen Abuja da Kaduna da Zamfara da jihar Maryland ta Amurka.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp