Home SIYASA Kotu ta Bayar da Umarnin Kwace Kadarorin Tsohon Gwamnan Zamfara Abdulaziz Yari

Kotu ta Bayar da Umarnin Kwace Kadarorin Tsohon Gwamnan Zamfara Abdulaziz Yari

Kotu ta Bayar da Umarnin Kwace Kadarorin Tsohon Gwamnan Zamfara Abdulaziz Yari

 

Hukumar ICPC mai binciken laifukan cin hanci da rashawa a Najeriya ta ce wata Babbar Kotun Tarayya a Abuja ta ba ta umarni na wucin gadi na kwace wasu kadarorin tsohon Gwamnan Jahar Zamfara Abdulaziz Yari.

Kaddarorin sun haɗa da gine-gine da kudaden da tsohon gwamnan ya ajiye a wasu bankunan kasar.

A yau Laraba alkalan kotun karkashin jagorancin Mai Shari’a Obiora Egwuatu ta bayar da umarnin kwace kadarorin, ciki har da wasu gine-gine 10 da ke ciki da wajen Najeriya.

Kakakin hukumar Misis Azuka Ogugua ta tabbatar wa BBC Hausa cewa wannan nasarar ta wucin gadi ce, kuma bayan lokacin da kotun ta diba, gwamnatin Najeriya na iya kwace kadarorin idan tsohon gwamnan ya kasa gamsar da kotu cewa ya mallaki su ta halaliyar hanya.

Ta ce: “Abin da wannan ke nufi shi ne bayan lokacin da kotun ta diba, kuma babu wanda ya iya gamsar da shari’a cewa ya mallaki kadarorin ta halattacciyar hanya, kotu za ta mika wa gwamnatin tarayya dukkan kadarorin na dindindin ke nan.”

Wannan hukuncin na zuwa ne bayan wani hukunci irinsa da wata babbar kotun ta yanke tana bayar da umarnin a kwace kusan naira miliyan 279 ciki har da dalolin Amurka da ta gano tsohon gwamnan ya mallaka ta haramtacciyar hanya.

Wasu cikin kadarorin da aka kwace suna manyan unguwanni a biranen Abuja da Kaduna da Zamfara da jihar Maryland ta Amurka.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp