Home Taska Tsohuwar Minista Mrs Sarah Ochekpe ta Magantu Kan Hukuncin da Kotu ta...

Tsohuwar Minista Mrs Sarah Ochekpe ta Magantu Kan Hukuncin da Kotu ta Yanke mata

Tsohuwar Minista Mrs Sarah Ochekpe ta Magantu Kan Hukuncin da Kotu ta Yanke mata

Mrs Sarah Ochekpe, Tsohuwar Ministan Albarkatun Ruwa ta kotu ta yanke wa hukuncin daurin shekaru 3 kan zargin karbar N450m ta ce bata gamsu da hukuncin ba.

Ochekpe da sauran mutanen biyu da aka yanke wa hukuncin sun ce sun umurci lauyoyinsu suyi nazarin hukuncin su sanar da su matakin da za su dauka.

Kotun ta saki Mrs Ochekpe ne da shugaban wucin gadi na PDP, Jihar Plateau, Hon Raymond Dabo da Leo Jitung bayan sun biya N1m

Tsohuwar Ministan Albarkatun Ruwa, Mrs Sarah Ochekpe ta ce bata gamsu ba da hukuncin babban kotun tarayya da ta yanke mata daurin shekaru uku da wasu mutane biyu kan zargin cire kudi Naira miliyan 450, wanda hakan ya saba ka’ida.

An yanke mata hukuncin tare da shugaban wucin gadi na PDP, Jihar Plateau, Hon Raymond Dabo da Leo Jitung kamar yadda The Sun ta rahoto.

a ce hukuncin da aka yi wanke su bisa zargin bannatar da kudi tunda an gano cewa sun mika kudin ga kwamitin yakin neman zabe na jihar.

Mai shari’a Musa Kurna na Babban Kotun Tarayya a Jos, wanda ya yanke hukuncin ya kuma ba su zabin biyan tara ta Naira miliyan 1.

Mrs Ochekpe, wacce ta yi martani kan hukuncin a St Jarlath Secondary School Bukuru, inda ta ke koyarwa ta ce ta bukaci lauyoyinta su yi nazarin hukuncin domin su bata shawarar matakin da za ta dauka, rahoton The Sun.

Ta bayyana cewa kowannensu ya biya Naira miliyan daya kuma an kyalle su su tafi gida.

Mrs Ochekpe ta yi bayanin abin da ya faru

Ochekpe ta ce EFCC ta gayyaci su zuwa ofishinta a Gombe a 2016, suka amsa gayyatar a Janairun 2017.

Ta ce dukkansu ba su san dalilin da yasa aka gayyace su ba amma jami’an EFCC sun fada musu ana zarginsu ne da rike kudin sata da ya kai Naira miliyan N450m.

“Mun rubuta takarda inda muka ce an yi zaben shugaban kasa da yan majalisar tarayya kuma an turo kudin ne daga Abuja zuwa Jihar Plateau.

“An zabi mutum uku su karbi kudin a madadin PDP na Jihar Plateau, kuma muka karba kudin ba tare da sanin akwai wata matsala ba.

“An bukaci mu bada bayanin kudaden da suka shiga asusun mu na baki sai suka yi ikirarin cewa kudin sata ne muka ce musu ba mu da masaniya kan hakan.”

Ta cigaba da cewa an dauko kudin daga banki kuma aka kai ofishin kamfen sannan mai ajiyan kudi ya tabbatar da hakan. Shugaban ALGON shima ya tabbatar an raba kudin domin zaben kananan hukumomi.

“Hakan yasa alkali ya wanke mu daga zargin. Amma aka fada mana cewa an same mu da laifin hadin baki kuma wai ba mu karba kudin ta hukumar da aka amince da rika hada-hadar kudi ba.

“An ci kowannen mu tarar N1m, muka biya sannan muka tafi gida. Mu dai ba mu gamsu da wannan hukuncin kuma mun fada wa lauyoyin mu kuma suna duba abin sannan su bamu shawarar abin da za mu yi,” in ji ta.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp