Home Taska Rikicin Ukraine da Rasha: ‘Yan Wasan Brazil Sun Roki Gwamnatin Kasarsu da...

Rikicin Ukraine da Rasha: ‘Yan Wasan Brazil Sun Roki Gwamnatin Kasarsu da ta Taimaka ta Kwashe su Daga Ukraine

Rikicin Ukraine da Rasha: ‘Yan Wasan Brazil Sun Roki Gwamnatin Kasarsu da ta Taimaka ta Kwashe su Daga Ukraine

Yan wasan Brazil da ke wasa a kungiyoyin Shakhtar Donetsk da Dynamo Kyiv sun roki gwamnatin kasarsu da ta taimaka ta kwashe su daga Ukraine.

Hakan ya biyo bayan hare-haren da Rasha ta fara kai wa Ukraine da safiyar Alhamis.

Wasu daga cikin yan wasan sun yada wani bidiyo a shafukan sada zumunta, inda suka bayyana halin da suke ciki tun bayan barkewar rikicin, da kuma bukatar hukumomin Brazil su taimaka su kwashe su tare da iyalansa daga Ukraine.

Dan wasan gaban Shakhtar Donetsk Junior Moraes ya rubuta a shafinsa na Instagram cewa ”halin da muke ciki ya yi muni. Ina so al’umma su yada wannan bidiyo har sai ya kai ga hukumonin Brazil.”

Ya kara da cewa ”an rufe kan iyakoki da bankuna, babu man fetur, kuma za a fuskanci karancin abinci da kudade a hannun jama’a.”

” Yan uwa da abokan arziki yanayin da muke ciki ya yi muni don mun makale a Kyiv muna neman mafita. Yanzu haka muna cikin wani otal ne. Ku taya mu da addu’a.” In ji Moraes.

Akwai akalla yan wasan Brazil 12 da ke wasa a kungiyar kwallon kafa ta Shakhtar, da suka hada da David Neres wanda bai dade da zuwa kungiyar ba daga Ajax da ke Holland.

Sauran yan wasan sun hada da Dodo, da Vitao, da Marlon, da Ismaily, da Vinicius Tobias, da Maycon, da Marcos Antonio, da Tete, da Alan Patrick, da Pedrinho da kuma Fernando.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp