Home Taska Rikicin Ukraine da Rasha: ‘Yan Wasan Brazil Sun Roki Gwamnatin Kasarsu da...

Rikicin Ukraine da Rasha: ‘Yan Wasan Brazil Sun Roki Gwamnatin Kasarsu da ta Taimaka ta Kwashe su Daga Ukraine

Rikicin Ukraine da Rasha: ‘Yan Wasan Brazil Sun Roki Gwamnatin Kasarsu da ta Taimaka ta Kwashe su Daga Ukraine

Yan wasan Brazil da ke wasa a kungiyoyin Shakhtar Donetsk da Dynamo Kyiv sun roki gwamnatin kasarsu da ta taimaka ta kwashe su daga Ukraine.

Hakan ya biyo bayan hare-haren da Rasha ta fara kai wa Ukraine da safiyar Alhamis.

Wasu daga cikin yan wasan sun yada wani bidiyo a shafukan sada zumunta, inda suka bayyana halin da suke ciki tun bayan barkewar rikicin, da kuma bukatar hukumomin Brazil su taimaka su kwashe su tare da iyalansa daga Ukraine.

Dan wasan gaban Shakhtar Donetsk Junior Moraes ya rubuta a shafinsa na Instagram cewa ”halin da muke ciki ya yi muni. Ina so al’umma su yada wannan bidiyo har sai ya kai ga hukumonin Brazil.”

Ya kara da cewa ”an rufe kan iyakoki da bankuna, babu man fetur, kuma za a fuskanci karancin abinci da kudade a hannun jama’a.”

” Yan uwa da abokan arziki yanayin da muke ciki ya yi muni don mun makale a Kyiv muna neman mafita. Yanzu haka muna cikin wani otal ne. Ku taya mu da addu’a.” In ji Moraes.

Akwai akalla yan wasan Brazil 12 da ke wasa a kungiyar kwallon kafa ta Shakhtar, da suka hada da David Neres wanda bai dade da zuwa kungiyar ba daga Ajax da ke Holland.

Sauran yan wasan sun hada da Dodo, da Vitao, da Marlon, da Ismaily, da Vinicius Tobias, da Maycon, da Marcos Antonio, da Tete, da Alan Patrick, da Pedrinho da kuma Fernando.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp