Home Taska Rikicin Ukraine da Rasha: ‘Yan Wasan Brazil Sun Roki Gwamnatin Kasarsu da...

Rikicin Ukraine da Rasha: ‘Yan Wasan Brazil Sun Roki Gwamnatin Kasarsu da ta Taimaka ta Kwashe su Daga Ukraine

Rikicin Ukraine da Rasha: ‘Yan Wasan Brazil Sun Roki Gwamnatin Kasarsu da ta Taimaka ta Kwashe su Daga Ukraine

Yan wasan Brazil da ke wasa a kungiyoyin Shakhtar Donetsk da Dynamo Kyiv sun roki gwamnatin kasarsu da ta taimaka ta kwashe su daga Ukraine.

Hakan ya biyo bayan hare-haren da Rasha ta fara kai wa Ukraine da safiyar Alhamis.

Wasu daga cikin yan wasan sun yada wani bidiyo a shafukan sada zumunta, inda suka bayyana halin da suke ciki tun bayan barkewar rikicin, da kuma bukatar hukumomin Brazil su taimaka su kwashe su tare da iyalansa daga Ukraine.

Dan wasan gaban Shakhtar Donetsk Junior Moraes ya rubuta a shafinsa na Instagram cewa ”halin da muke ciki ya yi muni. Ina so al’umma su yada wannan bidiyo har sai ya kai ga hukumonin Brazil.”

Ya kara da cewa ”an rufe kan iyakoki da bankuna, babu man fetur, kuma za a fuskanci karancin abinci da kudade a hannun jama’a.”

” Yan uwa da abokan arziki yanayin da muke ciki ya yi muni don mun makale a Kyiv muna neman mafita. Yanzu haka muna cikin wani otal ne. Ku taya mu da addu’a.” In ji Moraes.

Akwai akalla yan wasan Brazil 12 da ke wasa a kungiyar kwallon kafa ta Shakhtar, da suka hada da David Neres wanda bai dade da zuwa kungiyar ba daga Ajax da ke Holland.

Sauran yan wasan sun hada da Dodo, da Vitao, da Marlon, da Ismaily, da Vinicius Tobias, da Maycon, da Marcos Antonio, da Tete, da Alan Patrick, da Pedrinho da kuma Fernando.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp