Home Taska Gwamnatin Tarayya na Shirin Kwaso Daliban ‘Yan Najeriya Dake Zaune a Kasar...

Gwamnatin Tarayya na Shirin Kwaso Daliban ‘Yan Najeriya Dake Zaune a Kasar Ukraine

Gwamnatin Tarayya na Shirin Kwaso Daliban ‘Yan Najeriya Dake Zaune a Kasar Ukraine

Daliban Najeriya mazauna kasar Ukraniya sun kai kuka ga shugaba Buhari ya kwashesu cikin gaggawa.

Daliban sun aika wasikar kar ka kwana ga Buhari saboda an fara kai musu hare-hare a wuraren zamansu.

Gwamnatin tarayya da majalsar wakilai tuni sun yi alkawarin kwaso daliban.

Kungiyar daiban Najeriya dake karatu a kasar Ukraniya sun yi kira ga Shugaba Muhammadu Buhari yayi gaggawan kwashesu daga kasar.

Wannan ya biyo bayan yakin da ya barke tsakanin kasar Rasha da Ukraniya kuma kimanin mutum 50 sun mutu.

A wasikar mai taken, “BUKATA NA GAGGAWA GA SHUGABAN NAJERIYA MUHAMMADU BUHARI” da kungiyar ta aike ranar Alhamis, daliban sun bayyana yankunan da akwai yan Najeriya da aka kaiwa hari, rahoton DailyTrust.

Shugabar NANS dake Ukraniya, Eunice Eleaka, ta rattafu hannu, kan wasikar.

Wani sashen jawabin yace:

“Muna aike wannan wasika ne bisa rikicin Rasha da Ukraniya wanda yayi muni da safiyar nan 24 ga Febrairu 2022 inda aka fara tashin bama-bamai da harbe-harbe a wuraren da yan Najeriya ke zama.”

“Muna rokonka mai girma Shugaba MUHAMMADU BUHARI ka aiko a kwashe daliban Najeriya dake Ukraniya.”

Gwamnatin tarayya zata kwaso yan Najeriya dake zaune a kasar Ukraniya

Gwamnatin tarayya ta sanar da shirin da take yi na kwashe yan Najeriya dake zaune a Ukraniya sakamakon yakin da ya barke tsakanin kasar da Rasha a ranar Alhamis.

Gwamnati ta ce tana shirya jirgi na musamman da don kwaso su muddin aka bude tashohin jirgi.

Ministan harkokin wajen Najeriya, Geoffrey Onyeama, a hirar da yayi a tashar NTA yace an tuntubi ofishin jakadancin Najeriya dake Kiev kan shirya yadda za’a kwaso wadanda ke niyyar dawowa gida.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp