Home Taska Gwamnatin Tarayya na Shirin Kwaso Daliban ‘Yan Najeriya Dake Zaune a Kasar...

Gwamnatin Tarayya na Shirin Kwaso Daliban ‘Yan Najeriya Dake Zaune a Kasar Ukraine

Gwamnatin Tarayya na Shirin Kwaso Daliban ‘Yan Najeriya Dake Zaune a Kasar Ukraine

Daliban Najeriya mazauna kasar Ukraniya sun kai kuka ga shugaba Buhari ya kwashesu cikin gaggawa.

Daliban sun aika wasikar kar ka kwana ga Buhari saboda an fara kai musu hare-hare a wuraren zamansu.

Gwamnatin tarayya da majalsar wakilai tuni sun yi alkawarin kwaso daliban.

Kungiyar daiban Najeriya dake karatu a kasar Ukraniya sun yi kira ga Shugaba Muhammadu Buhari yayi gaggawan kwashesu daga kasar.

Wannan ya biyo bayan yakin da ya barke tsakanin kasar Rasha da Ukraniya kuma kimanin mutum 50 sun mutu.

A wasikar mai taken, “BUKATA NA GAGGAWA GA SHUGABAN NAJERIYA MUHAMMADU BUHARI” da kungiyar ta aike ranar Alhamis, daliban sun bayyana yankunan da akwai yan Najeriya da aka kaiwa hari, rahoton DailyTrust.

Shugabar NANS dake Ukraniya, Eunice Eleaka, ta rattafu hannu, kan wasikar.

Wani sashen jawabin yace:

“Muna aike wannan wasika ne bisa rikicin Rasha da Ukraniya wanda yayi muni da safiyar nan 24 ga Febrairu 2022 inda aka fara tashin bama-bamai da harbe-harbe a wuraren da yan Najeriya ke zama.”

“Muna rokonka mai girma Shugaba MUHAMMADU BUHARI ka aiko a kwashe daliban Najeriya dake Ukraniya.”

Gwamnatin tarayya zata kwaso yan Najeriya dake zaune a kasar Ukraniya

Gwamnatin tarayya ta sanar da shirin da take yi na kwashe yan Najeriya dake zaune a Ukraniya sakamakon yakin da ya barke tsakanin kasar da Rasha a ranar Alhamis.

Gwamnati ta ce tana shirya jirgi na musamman da don kwaso su muddin aka bude tashohin jirgi.

Ministan harkokin wajen Najeriya, Geoffrey Onyeama, a hirar da yayi a tashar NTA yace an tuntubi ofishin jakadancin Najeriya dake Kiev kan shirya yadda za’a kwaso wadanda ke niyyar dawowa gida.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp