Home Taska Gwamnatin Tarayya na Shirin Kwaso Daliban ‘Yan Najeriya Dake Zaune a Kasar...

Gwamnatin Tarayya na Shirin Kwaso Daliban ‘Yan Najeriya Dake Zaune a Kasar Ukraine

Gwamnatin Tarayya na Shirin Kwaso Daliban ‘Yan Najeriya Dake Zaune a Kasar Ukraine

Daliban Najeriya mazauna kasar Ukraniya sun kai kuka ga shugaba Buhari ya kwashesu cikin gaggawa.

Daliban sun aika wasikar kar ka kwana ga Buhari saboda an fara kai musu hare-hare a wuraren zamansu.

Gwamnatin tarayya da majalsar wakilai tuni sun yi alkawarin kwaso daliban.

Kungiyar daiban Najeriya dake karatu a kasar Ukraniya sun yi kira ga Shugaba Muhammadu Buhari yayi gaggawan kwashesu daga kasar.

Wannan ya biyo bayan yakin da ya barke tsakanin kasar Rasha da Ukraniya kuma kimanin mutum 50 sun mutu.

A wasikar mai taken, “BUKATA NA GAGGAWA GA SHUGABAN NAJERIYA MUHAMMADU BUHARI” da kungiyar ta aike ranar Alhamis, daliban sun bayyana yankunan da akwai yan Najeriya da aka kaiwa hari, rahoton DailyTrust.

Shugabar NANS dake Ukraniya, Eunice Eleaka, ta rattafu hannu, kan wasikar.

Wani sashen jawabin yace:

“Muna aike wannan wasika ne bisa rikicin Rasha da Ukraniya wanda yayi muni da safiyar nan 24 ga Febrairu 2022 inda aka fara tashin bama-bamai da harbe-harbe a wuraren da yan Najeriya ke zama.”

“Muna rokonka mai girma Shugaba MUHAMMADU BUHARI ka aiko a kwashe daliban Najeriya dake Ukraniya.”

Gwamnatin tarayya zata kwaso yan Najeriya dake zaune a kasar Ukraniya

Gwamnatin tarayya ta sanar da shirin da take yi na kwashe yan Najeriya dake zaune a Ukraniya sakamakon yakin da ya barke tsakanin kasar da Rasha a ranar Alhamis.

Gwamnati ta ce tana shirya jirgi na musamman da don kwaso su muddin aka bude tashohin jirgi.

Ministan harkokin wajen Najeriya, Geoffrey Onyeama, a hirar da yayi a tashar NTA yace an tuntubi ofishin jakadancin Najeriya dake Kiev kan shirya yadda za’a kwaso wadanda ke niyyar dawowa gida.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp