Home Taska Rikicin Rasha da Ukraine: ‘Yan Najeriya Sun Roki Shugaba Buhari ya Gargadi...

Rikicin Rasha da Ukraine: ‘Yan Najeriya Sun Roki Shugaba Buhari ya Gargadi Minista Lai Mohammed ya Kame Bakinsa Game da Lamarin

Air Comdr Yusuf Anas, Yushau Shuaib at the African Excellence Award in South-Africa
Air Comdr Yusuf Anas, Yushau Shuaib at the African Excellence Award in South-Africa

Rikicin Rasha da Ukraine: ‘Yan Najeriya Sun Roki Shugaba Buhari ya Gargadi Minista Lai Mohammed ya Kame Bakinsa Game da Lamarin

 

Ma’abota amfani da dandalin sada zumunta a Najeriya sun roki gwamnatin tarayya ta rufa wa kasar asiri ta yi shiru game da yakin Rasha da Ukraine.

Mutane da dama a dandalin sada zumuntan sun nuna fargabarsu kan abin da ka iya faruwa idan Najeriya ta tsoma bakinta duba da irin barazanar da Putin ya yi wa Amurka da NATO.

Wasu masu tsokacin sun roki Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya gargadi Minista Lai Mohammed ya kame bakinsa game da lamarin idan ba haka ba su bar kasar.

Wasu yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta sun shawarci gwamnatin tarayya ta ja bakinta ta yi shiru game da yakin da ake yi tsakanin Rasha da Ukraine, rahoton Vanguard.

Hakan na zuwa ne bayan Shugaban Rasha Vladmir Putin ya gargadi Amurka da NATO idan suka saka baki, ‘Rasha za ta mayar da martani nan take, kuma za ku fuskanci sakamakon da ba ku taba samu ba a tarihin ku.’

A lokacin hada wannan rahoton, kimanin sojojin Ukraine 137 ne suka mutu tun bayan da Rasha ta fara kutsa wa Ukraine a safiyar ranar Alhamis, sannan sojoji 316 sun jikkata.

Ga abin da wasu yan Najeriya ke cewa kamar yadda Vanguard ta tattaro:

Folorunsho Akin-Martins Odeyemi cewa ya yi:

“Ba na tunanin komai, kada dai gwamnatin mu ta saka baki domin Kawu Putin ainihin dan kungiyar asiri ne.”

Vincent John Ajakaiye ya ce:

“Don Allah wani ya shawarci Lai Mohammed kada ya ce komai domin idan ya yi magana zan kwashe kaya na in tafi Burkina-Fso domin samun zaman lafiya a rayuwa ta.”

Nkeiruka Best cewa ta yi:

“Ba mu gama tunanin yunwa da ke damun mu ba kuna son ku kara tunanin matsalar Rasha da Ukraine …

ko dai ba ku san abin da ya faru da mutumin farko da ya saka bakinsa a abin da babu ruwansa ne … idan kun ga dama su saka shugaban mu ya tsoma baki, za ku ji a jikinku.”

Shi kuma Okoro De MoneyMaker ya ce:

“Don Allah Buhari, saboda Najeriya ka fada wa Lai Mohammed kada ya yi tsokaci a kan wannan lamarin.”

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp