Home Taska Yadda Mai Shayi ya Halaka Kwastoman sa Saboda N10 a Jahar Ogun

Yadda Mai Shayi ya Halaka Kwastoman sa Saboda N10 a Jahar Ogun

Yadda Mai Shayi ya Halaka Kwastoman sa Saboda N10 a Jahar Ogun

 

Wani mai shayi mai suna Hamidu, yana hannun hukuma bayan ya halaka wani kwastoman shi a anguwar Arepo, karkashin karamar hukumar Obafemi Owode cikin Jihar Ogun.

An samu bayanai akan yadda kwastoman, mai suna Musa ya siya shayin N50 a wurin Hamidu ya biya shi N40, yayin neman cikon kudin, rikici ya barke tsakanin su.

Hamidu ya ka wa Musa naushi a kirji daga nan Musa ya fadi ba tare da ya shura ba, ya koma ga mahaliccin sa take anan hakan yasa aka kira ‘yan sanda suka wuce da Hamidu.

Jihar Ogun – Wani Hamidu mai shayi ya halaka kwastoman sa mai suna Musa akan N10 a anguwar Arepo da ke karkashin karamar hukumar Obafemi Owode cikin Jihar Ogun.

The Punch ta tattaro bayanai akan yadda Musa ya siya shayi a hannun Hamidu, maimakon ya biya shi N50 sai ya ba shi N40.

Saboda amsar cikon kudin ne rikicin ya barke musu suka dinga ba hammata iska.

Hamidu ya yi gaggawar naushin Musa a kirji wanda ya sa ya fadi kasa warwas.

Shugaban Odua People’s Congress (New Era), Olayiwola Ogunsolu ya sanar da wakilin The Punch yadda Musa ya mutu take yanke.

Yadda lamarin ya auku

Kamar yadda ya ce:

“Ranar Larabar da ta gabata, muna kasan gadar Arepo inda muka ji hayaniya wuraren anguwar Hausawa.

“Bayan isar mu wurin muka ga gawar mutumin. Bayan tambayar yadda lamarin ya auku, an sanar da mu cewa mai shayi ne ya halaka shi akan ya ki biyan N50 na kudin kofin shayi.

“Mun yi gaggawar sanar da ‘yan sanda wadanda suka zo suka wuce da mai shayin.”

Dan uwan mamacin ya shaida yadda Musa ya biya N40 maimakon N50 wanda hakan ya hassala mai shayin har ya yi masa aika-aikar.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar ya ce bai san komai dangane da lamarin ba

Shugaban Hausawa yankin, Usman Shehu ya ce bai san komai ba dangane da lamarin.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Abimbola Oyeyemi ya yi alkawarin sanar da wakilin The Punch idan ya samo bayanai.

Har aka kammala rubuta wannan rahoton bai tuntube shi ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp