Home SIYASA Rikicin Rasha da Ukraine: Gwamnatin Rasha ta Saki Jerin Sunayen Kasashen da...

Rikicin Rasha da Ukraine: Gwamnatin Rasha ta Saki Jerin Sunayen Kasashen da ba ta ga Maciji da su

Rikicin Rasha da Ukraine: Gwamnatin Rasha ta Saki Jerin Sunayen Kasashen da ba ta ga Maciji da su

 

Gwamnatin Rasha ta saki jerin sunayen kasashe da yankunan da ba ta ga maciji da su yayin da ta afka wa Ukraine da yaki.

Saboda takunkumin tattalin arziki da aka saka mata, tattalin arzikin kasar Rasha ya fara shiga matsala saboda kaurace mata da aka yi.

Rasha ta kutsa cikin kasar Ukraine a watan Fabrairu, amma dakarunta sun samu tsaiko saboda matsalar zirga-zirga da turjiyya daga sojojin Ukraine.

Moscow – Rasha a ranar Litinin 7 ga watan Maris ta wallafa jerin sunayen kasashen kasar waje da ta dauke su a matsayin wadanda ta ‘ki jini’, Newsweek ta rahoto.

Rasha ta ce daga yanzu ana bukatar izini na musamman daga gwamnati kafin a yi ko wane irin kasuwanci ne da kasashen, a wani martanin da ta yi na takunkumin karya tattalin arziki da aka saka mata kan kutsa wa cikin Ukraine.

Jerin kasashen da Rasha ta ce bata ga-maciji da su

Kasashe da yankunan da Rasha ta dauka a matsayin makiyanta sun hada da Australia, Albania, Andorra, the United Kingdom, Anguilla, British Virgin Islands, Gibraltar, Iceland, Canada, Liechtenstein, Micronesia, Monaco, New Zealand, Norway, da Taiwan.

sai an nemi izini daga gwamnati kafin a yi kasuwanci da kasashen, Gwamnatin Rasha

Ana bukatar izini daga wata hukuma ta Gwamnatin Rasha – Hukumar Kula da Hannun Jari na Kasashen Waje, wacce aka kafa a 2008 don saka ido kan hannun jari na kasashen waje ta sanar.

Sanarwar ta ce kamfanoni, yan kasuwa da mazauna Rasha za su rika biyan bashi da ake binsu na kasashen wajen ne ta hanyar amfani da rubles.

Wannan dokar ya shafi duk wata hada-hadar kudi da za a yi da ya kai rubles miliyan 10. Sanarwar ta kuma ce hukumar na gwamnatin Rasha da ke kula da saka hannun jari ce za ta rika bada izinin yin kasuwanci da yan kasar Rasha.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp