Home SIYASA Rikicin Rasha da Ukraine: Gwamnatin Rasha ta Saki Jerin Sunayen Kasashen da...

Rikicin Rasha da Ukraine: Gwamnatin Rasha ta Saki Jerin Sunayen Kasashen da ba ta ga Maciji da su

Rikicin Rasha da Ukraine: Gwamnatin Rasha ta Saki Jerin Sunayen Kasashen da ba ta ga Maciji da su

 

Gwamnatin Rasha ta saki jerin sunayen kasashe da yankunan da ba ta ga maciji da su yayin da ta afka wa Ukraine da yaki.

Saboda takunkumin tattalin arziki da aka saka mata, tattalin arzikin kasar Rasha ya fara shiga matsala saboda kaurace mata da aka yi.

Rasha ta kutsa cikin kasar Ukraine a watan Fabrairu, amma dakarunta sun samu tsaiko saboda matsalar zirga-zirga da turjiyya daga sojojin Ukraine.

Moscow – Rasha a ranar Litinin 7 ga watan Maris ta wallafa jerin sunayen kasashen kasar waje da ta dauke su a matsayin wadanda ta ‘ki jini’, Newsweek ta rahoto.

Rasha ta ce daga yanzu ana bukatar izini na musamman daga gwamnati kafin a yi ko wane irin kasuwanci ne da kasashen, a wani martanin da ta yi na takunkumin karya tattalin arziki da aka saka mata kan kutsa wa cikin Ukraine.

Jerin kasashen da Rasha ta ce bata ga-maciji da su

Kasashe da yankunan da Rasha ta dauka a matsayin makiyanta sun hada da Australia, Albania, Andorra, the United Kingdom, Anguilla, British Virgin Islands, Gibraltar, Iceland, Canada, Liechtenstein, Micronesia, Monaco, New Zealand, Norway, da Taiwan.

sai an nemi izini daga gwamnati kafin a yi kasuwanci da kasashen, Gwamnatin Rasha

Ana bukatar izini daga wata hukuma ta Gwamnatin Rasha – Hukumar Kula da Hannun Jari na Kasashen Waje, wacce aka kafa a 2008 don saka ido kan hannun jari na kasashen waje ta sanar.

Sanarwar ta ce kamfanoni, yan kasuwa da mazauna Rasha za su rika biyan bashi da ake binsu na kasashen wajen ne ta hanyar amfani da rubles.

Wannan dokar ya shafi duk wata hada-hadar kudi da za a yi da ya kai rubles miliyan 10. Sanarwar ta kuma ce hukumar na gwamnatin Rasha da ke kula da saka hannun jari ce za ta rika bada izinin yin kasuwanci da yan kasar Rasha.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp