Home Taska Bani na Kashe ta ba: Kotu ta yi Watsi da Ikirarin Makashin...

Bani na Kashe ta ba: Kotu ta yi Watsi da Ikirarin Makashin Hanifa Abubakar

Bani na Kashe ta ba: Kotu ta yi Watsi da Ikirarin Makashin Hanifa Abubakar

 

Babbar Kotun Kano ta yi watsi da ikirarin shugaban makarantar su Hanifa Abubakar, Abdulmalik Tanko.

Tanko, wanda da farko ya amsa cewa ya kashe Hanifa, ya bukaci Kotu ta yi watsi da maganarsa domin ya faɗeta ne don tsirar da rayuwarsa.

Sai dai alkalin Kotun, Mai Shari’a Usman Na’abba, ya ce bai gamsu da hujjojin Tanko ba, dan haka ya karbi cewa ba’a tursasa masa ba.

Kano – Babbar Kotun jihar Kano ta fara shirin yanke hukunci game da shari’ar kisan Hanifa Abubakar yar kimanin shekara biyar a duniya, kamar yadda Aminiya ta ruwaito.

Kotun ta yi watsi da ikirarin wanda ake zargi na farko, Abdulmalik Tanko, wanda ya canza maganarsa ta farko, inda ya ce ba shi ne ya kashe Hanifa ba.

Rahoto ya nuna cewa yanzu haka, Kotun ƙarkashin jagorancin mai shari’a Usman Na’abba, na shirin yanke hukunci kan kisan daliba Hanifa.

Alƙalin Kotun na shirin yanke hukunci ne bayan gamsuwa da cewa babu wanda ya tilasta wa wanda ake zargi, shugaban makaranta, Abdulmalik Tanko, ya amince shi ya kashe yarinyar.

Tun da farko Tanko ya roki Kotun ta yi watsi da kalamansa na farko da ya amsa kisan Hanifa, ya kuma kafa hujja da cewa ya yi haka ne domin ceton rayuwarsa daga azabtarwan yan sanda.

Yayin zaman cigaba da sauraron ƙarar, Tanko ya shaida wa Kotu yadda yan sanda suka rinka azabtar da shi kuma suka masa barazanar kisa matukar bai amsa laifin da ake tuhumarsa ba.

Sai dai bayanan Tanko ya saɓa wa na matar da ake zargin su tare, Fatima Jibrin, wacce ta bayyana cewa masu binciken sun ba ta tsoro amma ba su doke ta ba.

A nasu bangare, yan sandan da suka gudanar da bincike sun musanta zargin Tanko, tare da faɗa wa Kotu cewa sun bi hanyoyin da ya dace wajen karban bayanan mutanen da ake zargin.

Kotu ta yi watsi da ikirarin Tanko Mai Shari’a Na’abba, ya yi watsi da ikirarin Tanko, inda yace bai kawo hujjojin da zasu gamsar da Kotu cewa an tursasa masa ba wajen bincike.

Alƙalin ya ce:

“Na gamsu cewa an bi hanyoyin da ya dace wajen karɓan bayanan mutum biyu na farko da ake zargi kuma da yardarsu, saboda haka na karbi bayanan.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp