Home SIYASA Shugaba Buhari ya Nada Sabon Shugaban HYPREP

Shugaba Buhari ya Nada Sabon Shugaban HYPREP

Shugaba Buhari ya Nada Sabon Shugaban HYPREP

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin jami’in da zai shugabanci aikin HYPREP.

Giadom Ferdinand Dumbari zai rike shugabancin HYPREP tun daga yanzu har zuwa shekarar 2026.

Dr. Giadom Dumbari kwararre ne a bangaren ma’adanai, kuma babban malami ne a jami’ar UNIPORT.

FCT, Abuja – Mai girma shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin Giadom Ferdinand Dumbari a matsayin wanda zai kula da aikin HYPREP.

Wannan sanarwa ta fito ne daga bakin ma’aikatar muhalli na tarayya a ranar Talata, 8 ga watan Maris 2022. Jaridar nan ta The Cable ta fitar da wannan rahoton.

Dr. Giadom Ferdinand Dumbari zai shafe shekaru hudu yana wannan aiki na magance illar gurbacewar wuri da ake samu a dalilin sinadaran ‘Hydrocarbons’.

Kamar yadda sanarwar ta bayyana, Ferdinand Dumbari ya samu Digirin farko a ilmin ma’adanan kasa a jami’ar Fatakwal da M. Phil a jami’ar jiha duk a Ribas din.

A wannan jami’ar tarayya da ke Fatakwal ne Giadom Ferdinand Dumbari ya yi PhD a fannin ma’adanai. Malamin jami’ar ya yi rubuce kusan 30 a bangarensa.

Masani a wannan harka

Sabon shugaban na HYPREP ya shafe sama da shekaru 20 yana nazari da bincike a kan hadarin wadannan ‘Hydrocarbons’ da manyan karafuna da sauran sinadarai.

A ciken irin nazarin da Ferdinand Dumbari ya yi, ya duba yadda sinadaran suke gurbata Ruwan kasa. Legit.ng ta fahimci hakan ta sa yake ba UNEP shawara tun 2019.

Jaridar Independent ta ce kafin wannan nadin mukami da aka ba shi, Dr. Ferdinand Dumbari kwararren ma’aikaci ne da yake aiki da UNEP a yankin Ogoniland.

Bugu da kari, Dr. Dumbari yana cikin kungiyoyin kwararrun masana a kan harkar ma’adanai na kasa. Sannan ya yi aiki da gwamnatin Ribas, NDDC, da kamfanin NDPD.

Ya cancanci ya rike HYPREP

Mun samu labari cewa shugaban na HYPREP ya rike mataimakin shugaba na aikin Shell PER DEC COY, don haka wani abokin aikinsa ya ce lallai ya cancanta.

Wannan jami’in NSCDC da ya yi aiki da shi a Fatakwal ya ce shakka babu Dr. Dumbari ya dace da wannan mukami domin kuwa an dauko wanda ya san bakin zaren.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp