Home SIYASA Shugaba Buhari ya Nada Sabon Shugaban HYPREP

Shugaba Buhari ya Nada Sabon Shugaban HYPREP

Shugaba Buhari ya Nada Sabon Shugaban HYPREP

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin jami’in da zai shugabanci aikin HYPREP.

Giadom Ferdinand Dumbari zai rike shugabancin HYPREP tun daga yanzu har zuwa shekarar 2026.

Dr. Giadom Dumbari kwararre ne a bangaren ma’adanai, kuma babban malami ne a jami’ar UNIPORT.

FCT, Abuja – Mai girma shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin Giadom Ferdinand Dumbari a matsayin wanda zai kula da aikin HYPREP.

Wannan sanarwa ta fito ne daga bakin ma’aikatar muhalli na tarayya a ranar Talata, 8 ga watan Maris 2022. Jaridar nan ta The Cable ta fitar da wannan rahoton.

Dr. Giadom Ferdinand Dumbari zai shafe shekaru hudu yana wannan aiki na magance illar gurbacewar wuri da ake samu a dalilin sinadaran ‘Hydrocarbons’.

Kamar yadda sanarwar ta bayyana, Ferdinand Dumbari ya samu Digirin farko a ilmin ma’adanan kasa a jami’ar Fatakwal da M. Phil a jami’ar jiha duk a Ribas din.

A wannan jami’ar tarayya da ke Fatakwal ne Giadom Ferdinand Dumbari ya yi PhD a fannin ma’adanai. Malamin jami’ar ya yi rubuce kusan 30 a bangarensa.

Masani a wannan harka

Sabon shugaban na HYPREP ya shafe sama da shekaru 20 yana nazari da bincike a kan hadarin wadannan ‘Hydrocarbons’ da manyan karafuna da sauran sinadarai.

A ciken irin nazarin da Ferdinand Dumbari ya yi, ya duba yadda sinadaran suke gurbata Ruwan kasa. Legit.ng ta fahimci hakan ta sa yake ba UNEP shawara tun 2019.

Jaridar Independent ta ce kafin wannan nadin mukami da aka ba shi, Dr. Ferdinand Dumbari kwararren ma’aikaci ne da yake aiki da UNEP a yankin Ogoniland.

Bugu da kari, Dr. Dumbari yana cikin kungiyoyin kwararrun masana a kan harkar ma’adanai na kasa. Sannan ya yi aiki da gwamnatin Ribas, NDDC, da kamfanin NDPD.

Ya cancanci ya rike HYPREP

Mun samu labari cewa shugaban na HYPREP ya rike mataimakin shugaba na aikin Shell PER DEC COY, don haka wani abokin aikinsa ya ce lallai ya cancanta.

Wannan jami’in NSCDC da ya yi aiki da shi a Fatakwal ya ce shakka babu Dr. Dumbari ya dace da wannan mukami domin kuwa an dauko wanda ya san bakin zaren.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp