Home SIYASA Majalisar Dattawa ta yi Watsi da Kudurin Dokar Zabe da Shugaba Buhari...

Majalisar Dattawa ta yi Watsi da Kudurin Dokar Zabe da Shugaba Buhari ya Gabatar

Majalisar Dattawa ta yi Watsi da Kudurin Dokar Zabe da Shugaba Buhari ya Gabatar

Majalisar Dattawa ta yi watsi da kudurin dokar zabe da shugaba Buhari ya gabatar saboda wasu dalilai.

A baya majalisar ta fusata da jin yadda kotu ta ba da umarni gareta cewa, kada ta sake ta gyara dokar zaben.

A yau dai majalisar ta kawo karshen magana, ta kada kuri’a kuma an yi watsi da dokar gabanin karatu na biyu.

FCT, Abuja – Jaridar The Nation ta ruwaito cewa, majalisar dattawa a ranar Laraba ta yi watsi da kudirin doka da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya gabatar na neman gyara dokar zabe ta 2022.

Kudirin doka mai taken: “Kudirin dokar da zai gyara dokar zabe ta 2022 da kuma abubuwa masu alaka, 2022,” Sanatoci sun yi watsi da shi, lamarin da ya dakatar da karatun kudurin na biyu.

Kudurin dokar ya tsallake karatu na farko a ranar Talata duk da umarnin da kotu ta bayar na hana Majalisar Dattawa yin aiki akansa.

Shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan ya kalubalanci hukuncin kotun yana mai cewa a kowane hali, bangaren shari’a bai da ikon hana majalisar gudanar da ayyukanta na tsarin mulki.

Kafin Majalisar Dattawa ta fara nazarin kudirin a ranar Laraba, Sanata Adamu Aliero, yayin da yake karanto doka ta 52 (5) na Majalisar Dattawa, ya bukaci Shugaban Majalisar da ya yi watsi da shawarar duba ga kudirin.

Sai dai Lawan ya dage. Ya sake jaddada matsayinsa na cewa Sanatoci ne ke da hakkin kin amincewa da kudirin ba bangaren shari’a da ke neman hana majalisar gudanar da ayyukanta ba.

Saboda haka, Sanatoci sun kada kuri’ar kin amincewa da kudirin na hana sake karanta shi a karo na biyu.

Karin bayani na nan tafe…

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp