Home SIYASA Majalisar Dattawa ta yi Watsi da Kudurin Dokar Zabe da Shugaba Buhari...

Majalisar Dattawa ta yi Watsi da Kudurin Dokar Zabe da Shugaba Buhari ya Gabatar

Majalisar Dattawa ta yi Watsi da Kudurin Dokar Zabe da Shugaba Buhari ya Gabatar

Majalisar Dattawa ta yi watsi da kudurin dokar zabe da shugaba Buhari ya gabatar saboda wasu dalilai.

A baya majalisar ta fusata da jin yadda kotu ta ba da umarni gareta cewa, kada ta sake ta gyara dokar zaben.

A yau dai majalisar ta kawo karshen magana, ta kada kuri’a kuma an yi watsi da dokar gabanin karatu na biyu.

FCT, Abuja – Jaridar The Nation ta ruwaito cewa, majalisar dattawa a ranar Laraba ta yi watsi da kudirin doka da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya gabatar na neman gyara dokar zabe ta 2022.

Kudirin doka mai taken: “Kudirin dokar da zai gyara dokar zabe ta 2022 da kuma abubuwa masu alaka, 2022,” Sanatoci sun yi watsi da shi, lamarin da ya dakatar da karatun kudurin na biyu.

Kudurin dokar ya tsallake karatu na farko a ranar Talata duk da umarnin da kotu ta bayar na hana Majalisar Dattawa yin aiki akansa.

Shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan ya kalubalanci hukuncin kotun yana mai cewa a kowane hali, bangaren shari’a bai da ikon hana majalisar gudanar da ayyukanta na tsarin mulki.

Kafin Majalisar Dattawa ta fara nazarin kudirin a ranar Laraba, Sanata Adamu Aliero, yayin da yake karanto doka ta 52 (5) na Majalisar Dattawa, ya bukaci Shugaban Majalisar da ya yi watsi da shawarar duba ga kudirin.

Sai dai Lawan ya dage. Ya sake jaddada matsayinsa na cewa Sanatoci ne ke da hakkin kin amincewa da kudirin ba bangaren shari’a da ke neman hana majalisar gudanar da ayyukanta ba.

Saboda haka, Sanatoci sun kada kuri’ar kin amincewa da kudirin na hana sake karanta shi a karo na biyu.

Karin bayani na nan tafe…

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp