Home Taska Dakarun ‘Yan Sandan Jahar Kaduna Sun Kama ‘Yan Bindiga 200 da ‘Yan...

Dakarun ‘Yan Sandan Jahar Kaduna Sun Kama ‘Yan Bindiga 200 da ‘Yan Fashi 20 a Faɗin Jahar

Raymond Dokpesi of AIT
Raymond Dokpesi of AIT

Dakarun ‘Yan Sandan Jahar Kaduna Sun Kama ‘Yan Bindiga 200 da ‘Yan Fashi 20 a Faɗin Jahar

Rundunar yan sanda ta jihar Kaduna tace ta samu nasarar yin ram da yan bindiga 200, yan fashi 20 a faɗin jihar.

Kakakin yan sandan ya kuma bayyana cewa hukumar ta kwato makamai da yawa duk a tsakanin watan Janairu zuwa Maris.

Ya ce namijin kokarin da yan sanda suka yi tun bayan kama aikin kwamishina shi ne sanadin samun zaman lafiya a jihar.

Kaduna – Rundunar yan sanda reshen jihar Kaduna tace dakarunta sun samu nasarar damke mutum 200 da ake zargin yan bindiga ne da yan fashi da makami 20 tsakanin watan Janairu zuwa Maris.

Kakakin yan sanda na jihar, ASP Mohammed Jalige, shi ne ya faɗi haka a taron manema labarai a hedkwatar hukumar, ranar Laraba a Kaduna, kamar yadda The Nation ta rahoto.

Jalige ya bayyana cewa hukumarsu ta kwato bindigun AK47 guda 18, Alburusai 2000 kala daban-daban, kananan bindigun hannu 10, Motoci 10, babura 9 da sauran makamai.

A kalamansa da Channels tv ta rahoto, kakakin yan sandan ya ce:

“Mun saba gana wa da ku lokaci bayan lokaci domin bayyana nasarorin da muka samu a yaƙi da ta’addancin yan bindiga, garkuwa da mutane da sauran manyan laifukan da suka shafi al’umma.”

“Hukumar yan sanda a tsawon wannan lokacin da muke magana tana sane da tabarbarewar kalubalen da suka addabi jihar nan da suka haɗa da harin yan bindiga, garkuwa, fashi da makami, rikicin makiyaya da manoma.”

“Mun yi iyakar bakin kokari wajen magance waɗan nan matsaloli kuma sanadin haka ne aka samu zaman lafiyan da mutane ke jin dadi a yanzun.”

Jalige ya ƙara da cewa lokacin da sabon kwamishinan yan sanda na Kaduna, Mudassiru Abdullahi, ya kama aiki, watanni kaɗan da suka wuce, jihar ta fuskanci kalubalen tsaro mai tsanani.

“Bisa goyon baya da taimakon sufeta janar na yan sandan kasa, da gwamnatin Kaduna, dakarun yan sanda sun jajirce wajen daƙile kalubalen tsaro, wanda yanzu mutanen yankuna suka samu sa’ida.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp