Home Taska Bayan Karbar Kudin Fansa N1m: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutumin da Suka...

Bayan Karbar Kudin Fansa N1m: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutumin da Suka Sace a Jahar Kaduna

Bayan Karbar Kudin Fansa N1m: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutumin da Suka Sace a Jahar Kaduna

 

‘Yan bindiga sun halaka wani bawan Allah da suka sace bayan sun karbe kudin fansa.

Labarin mutuwar ya zo ne a daren Talata bayan yan uwan marigayin sun kai ma yan bindigar naira miliyan daya da suka bukata.

Har yanzu akwai sauran mutanen da aka sace su tare a hannun yan bindigar ciki harda wata mai shirin zama amarya.

Kaduna– Yan bindiga sun kashe wani mutum da suka sace bayan sun karbi naira miliyan daya a matsayin kudin fansa daga yan uwansa, Daily Trust ta rahoto.

A watan Fabrairu ne yan bindiga suka farmaki gidan mutumin a yankin Rigachikun da ke karamar hukumar Igabi sannan suka sace shi da wasu a yankin ciki harda mai shirin zama amarya.

A yayin mamayar, an harbe wani jami’in kwastam da ke aiki da FOU Zone B, Kaduna sannan daga bisani ya mutu a asibiti.

Wata mata a yankin ta fada ma Daily Trust cewa labarin mutuwar mutumin ya zo ne a daren Talata bayan yan uwan marigayin sun kai ma yan bindigar kudin fansa.

Ta ce:

“Sun harbe shi bayan sun karbi kudin fansa daga mutumin da ya kai masu kudin. Dukkanin mazauna yankin na cikin alhini bayan sun sami labarin mutuwar.”

An tattaro cewa an yi jana’izar mutumin a garin Unguwar Shanu inda iyalansa ke da zama.

Dailypost ta kuma rahoto cewa har yanzu amaryar da wani mutum daya suna a hannun wadanda suka yi garkuwa da su din.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp