Home Taska Bayan Karbar Kudin Fansa N1m: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutumin da Suka...

Bayan Karbar Kudin Fansa N1m: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutumin da Suka Sace a Jahar Kaduna

Bayan Karbar Kudin Fansa N1m: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutumin da Suka Sace a Jahar Kaduna

 

‘Yan bindiga sun halaka wani bawan Allah da suka sace bayan sun karbe kudin fansa.

Labarin mutuwar ya zo ne a daren Talata bayan yan uwan marigayin sun kai ma yan bindigar naira miliyan daya da suka bukata.

Har yanzu akwai sauran mutanen da aka sace su tare a hannun yan bindigar ciki harda wata mai shirin zama amarya.

Kaduna– Yan bindiga sun kashe wani mutum da suka sace bayan sun karbi naira miliyan daya a matsayin kudin fansa daga yan uwansa, Daily Trust ta rahoto.

A watan Fabrairu ne yan bindiga suka farmaki gidan mutumin a yankin Rigachikun da ke karamar hukumar Igabi sannan suka sace shi da wasu a yankin ciki harda mai shirin zama amarya.

A yayin mamayar, an harbe wani jami’in kwastam da ke aiki da FOU Zone B, Kaduna sannan daga bisani ya mutu a asibiti.

Wata mata a yankin ta fada ma Daily Trust cewa labarin mutuwar mutumin ya zo ne a daren Talata bayan yan uwan marigayin sun kai ma yan bindigar kudin fansa.

Ta ce:

“Sun harbe shi bayan sun karbi kudin fansa daga mutumin da ya kai masu kudin. Dukkanin mazauna yankin na cikin alhini bayan sun sami labarin mutuwar.”

An tattaro cewa an yi jana’izar mutumin a garin Unguwar Shanu inda iyalansa ke da zama.

Dailypost ta kuma rahoto cewa har yanzu amaryar da wani mutum daya suna a hannun wadanda suka yi garkuwa da su din.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp