Home Taska Yadda Mutane 18 Suka Tsallake Rijiya da Baya a Jahar Kwara

Yadda Mutane 18 Suka Tsallake Rijiya da Baya a Jahar Kwara

Yadda Mutane 18 Suka Tsallake Rijiya da Baya a Jahar Kwara

Allah ya kawo wani lamarin wuta da sauki yayin da wata Motar Bus dake tsakar tafiya a kan titi makare da mutane ta kama da wuta.

Mutum 18 dake cikin motar sun samu nasarar tsira daga lamarin, amma kayan su baki ɗaya sun kone kurmus a ciki.

Kwamandan hukumar kare haɗurra na jihar Kwara ya ce dole ta sa suka tsayar da motoci a kan hanyar domin shawo kan wutar.

Kwara– Wasu mutane 18 sun ga tashin hankali kuma lamarin ya zo da sauƙi yayin da Motar Bus mai ɗaukar mutum 18 da suke ciki ta kama da wuta ta cikin zabga gudu.

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa, lamarin wanda ya auku a ƙauyen Koko Araromi, kan hanyar Ajase Ipo, jihar Kwara ya bar matafiya da direbobi a tsaye.

Motar Bas ɗin, wacce rahoto ya nuna cewa tana kan hanyar zuwa garin Osdogbo a jihar Osun ta kama da wuta ne da misalin ƙarfe 10:57 na safe ana cikin zabga tafiya.

Allah ya kawo abun da sauki, domin duk da ba’a rasa rayuka ba kasancewar Mutanen cikin motar sun yi gaggawar fita, amma duk kan kayan su da suke tafe da su a motar sun kone kurmus.

Wane matakin hukumomi suka ɗauka?

Shugaban rundunar hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa (FRSC) reshen jihar Kwara, Jonathan Owoade, ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai a wata hira ta wayar salula.

Owoade wanda ya alaƙanta kama wutar motar da yoyon man Fetur ɗin motar, ya bayyana cewa:

“Jami’an hukumar kare haɗurra FRSC sun ɗauki matakin dakatar da motoci masu tafiya a kan hanyar na tsawon mintuna saboda wutar dake ci a Bas ɗin, hakan ya zame musu wajibi.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp