Home Taska Yadda Mutane 18 Suka Tsallake Rijiya da Baya a Jahar Kwara

Yadda Mutane 18 Suka Tsallake Rijiya da Baya a Jahar Kwara

Yadda Mutane 18 Suka Tsallake Rijiya da Baya a Jahar Kwara

Allah ya kawo wani lamarin wuta da sauki yayin da wata Motar Bus dake tsakar tafiya a kan titi makare da mutane ta kama da wuta.

Mutum 18 dake cikin motar sun samu nasarar tsira daga lamarin, amma kayan su baki ɗaya sun kone kurmus a ciki.

Kwamandan hukumar kare haɗurra na jihar Kwara ya ce dole ta sa suka tsayar da motoci a kan hanyar domin shawo kan wutar.

Kwara– Wasu mutane 18 sun ga tashin hankali kuma lamarin ya zo da sauƙi yayin da Motar Bus mai ɗaukar mutum 18 da suke ciki ta kama da wuta ta cikin zabga gudu.

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa, lamarin wanda ya auku a ƙauyen Koko Araromi, kan hanyar Ajase Ipo, jihar Kwara ya bar matafiya da direbobi a tsaye.

Motar Bas ɗin, wacce rahoto ya nuna cewa tana kan hanyar zuwa garin Osdogbo a jihar Osun ta kama da wuta ne da misalin ƙarfe 10:57 na safe ana cikin zabga tafiya.

Allah ya kawo abun da sauki, domin duk da ba’a rasa rayuka ba kasancewar Mutanen cikin motar sun yi gaggawar fita, amma duk kan kayan su da suke tafe da su a motar sun kone kurmus.

Wane matakin hukumomi suka ɗauka?

Shugaban rundunar hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa (FRSC) reshen jihar Kwara, Jonathan Owoade, ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai a wata hira ta wayar salula.

Owoade wanda ya alaƙanta kama wutar motar da yoyon man Fetur ɗin motar, ya bayyana cewa:

“Jami’an hukumar kare haɗurra FRSC sun ɗauki matakin dakatar da motoci masu tafiya a kan hanyar na tsawon mintuna saboda wutar dake ci a Bas ɗin, hakan ya zame musu wajibi.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp