Home Taska Yadda Mutane 18 Suka Tsallake Rijiya da Baya a Jahar Kwara

Yadda Mutane 18 Suka Tsallake Rijiya da Baya a Jahar Kwara

Yadda Mutane 18 Suka Tsallake Rijiya da Baya a Jahar Kwara

Allah ya kawo wani lamarin wuta da sauki yayin da wata Motar Bus dake tsakar tafiya a kan titi makare da mutane ta kama da wuta.

Mutum 18 dake cikin motar sun samu nasarar tsira daga lamarin, amma kayan su baki ɗaya sun kone kurmus a ciki.

Kwamandan hukumar kare haɗurra na jihar Kwara ya ce dole ta sa suka tsayar da motoci a kan hanyar domin shawo kan wutar.

Kwara– Wasu mutane 18 sun ga tashin hankali kuma lamarin ya zo da sauƙi yayin da Motar Bus mai ɗaukar mutum 18 da suke ciki ta kama da wuta ta cikin zabga gudu.

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa, lamarin wanda ya auku a ƙauyen Koko Araromi, kan hanyar Ajase Ipo, jihar Kwara ya bar matafiya da direbobi a tsaye.

Motar Bas ɗin, wacce rahoto ya nuna cewa tana kan hanyar zuwa garin Osdogbo a jihar Osun ta kama da wuta ne da misalin ƙarfe 10:57 na safe ana cikin zabga tafiya.

Allah ya kawo abun da sauki, domin duk da ba’a rasa rayuka ba kasancewar Mutanen cikin motar sun yi gaggawar fita, amma duk kan kayan su da suke tafe da su a motar sun kone kurmus.

Wane matakin hukumomi suka ɗauka?

Shugaban rundunar hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa (FRSC) reshen jihar Kwara, Jonathan Owoade, ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai a wata hira ta wayar salula.

Owoade wanda ya alaƙanta kama wutar motar da yoyon man Fetur ɗin motar, ya bayyana cewa:

“Jami’an hukumar kare haɗurra FRSC sun ɗauki matakin dakatar da motoci masu tafiya a kan hanyar na tsawon mintuna saboda wutar dake ci a Bas ɗin, hakan ya zame musu wajibi.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp