Home Taska ‘Yan Sandan Najeriya Sun Kama Kasurgumin Mai Garkuwa da Mutane a Hanyar...

‘Yan Sandan Najeriya Sun Kama Kasurgumin Mai Garkuwa da Mutane a Hanyar Abuja-Kaduna

‘Yan Sandan Najeriya Sun Kama Kasurgumin Mai Garkuwa da Mutane a Hanyar Abuja-Kaduna

Yan sanda a Najeriya sun ce sun kama wani da ake zargin kasurgumin mai garkuwa da mutane ne tare da wasu mutum 29 na daban,

‘Yan sandan sun ce mutane suna da hannu a yawancin garkuwar da ake yi da mutane da fashi da makami wadanda suka fi mayar da hankali a kan hanyar Abuja-Kaduna har da ma cikin Kaduna.

Mutumin mai shekara 36 ya amsa cewa shi yake jagorantar kungiyar, cikin wata sanarwa da ‘yan sanda suka fitar a yammacin Alhamis.

Hanyar Abuja-Kaduna na daya daga cikin hanyoyi masu matukar hadari a Najeriya yayin da masu garkuwa da mutane ke yi wa matafiya kwantan bauna a hanyar.

Sau da yawa ke kama harbin kan mai uwa da wabi domin tursasa musu tsayawa a hanya.

An kashe matafiya da yawa a hatsaniya wadanda kuma suka tsira sai a yi garkuwa da su kuma ana sakinsu ne bayan sun biya kudaden fansa.

Wannan dalili ya tilastawa mutane da dama daina bin hanyar suka koma jirgin kasa – wanda suke ganin hakan a matsayin wani tudun mun tsira daga bin hanyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp