Home Taska Tsohuwar Ministar Buhari ta Bayyana Yadda ta Ci gaba da Rayuwa Bayan...

Tsohuwar Ministar Buhari ta Bayyana Yadda ta Ci gaba da Rayuwa Bayan Badakatar kwalin NYSC

Tsohuwar Ministar Buhari ta Bayyana Yadda ta Ci gaba da Rayuwa Bayan Badakatar kwalin NYSC

Kemi Adeosun ta bayyana irin halin da ta riski kanta a ciki bayan badakatar satifiket dinta.

Tsohuwar ministar ta bayyana cewa bayan afkuwar lamarin ta kan yi kuka a kullun kwanan duniya har tsawon watanni uku.

Ta ce ta shiga kuncin rayuwa ta yadda take jinta kamar a cikin mummunan rami ba tare da aiki ba.

Tsohuwar ministar kudi, Misis Kemi Adeosun, ta fito ta bayyana yadda ta ci gaba da rayuwa bayan badakatar kwalin NYSC.

Punch ta rahoto cewa Adeosun ta ce kullun sai ta yi kuka ba tare da aiki ba tsawon watanni uku.

Adeosun, wacce ta magantu a bikin cika shekaru 10 na taron mata wanda cocin the Jesus House Church, United Kingdom ta shirya, ta yi bayanin cewa ji tayi kamar ta fada cikin wani mummunan rami.

A cewarta, komai game da rayuwarta ya tsaya cak yayin da take fama da jin kunya, cin amana, bakin ciki da tozarta.

Ta ce:

“Wannan lokaci na rayuwa ya kasance mai matukar wahala a gare ni. Na je na shiga yanayi irin na Ngozi Okonjo-Iweala. Don haka, na sha caccaka tun daga ranar farko, yanayin yay i kamar abubuwa basa tafiya daidai. Kwatsam sai tattalin arziki ya fara inganta. Kamar na fara ganin sakamakon da ake so. Daga nan kuma sai ga wata badakalar takardar shedar ta zo. Kuma kafin in ankara komai ya juye. Kuma haka lamarin ya yi fice.”

Adeosun ta ce abun bakin ciki ne cewa bata iya fadin nata bangaren na labarin ba sannan dole ta yi murabus a lokacin da ta ga ba za ta iya jure lamarin ba.

Tsohuwar ministar ta ce:

“An haife ni kuma na tashi a Burtaniya; hakika gidan iyayena na a Landan. Ziyarar da na kawo Najeriya har na kai shekara 34 hutu ne, da bizan da na samu a fasfot dina na Burtaniya. Lokacin da na gama makaranta, a lokacin babu damar zama yar kasa biyu; Ko dai na yi watsi da zama yar kasar Burtaniya ko kuma in rike shi kuma in yi aiki a nan. Ban yi watsi da nawa ba. Na gama makaranta ina da shekaru 21 kuma na fara aiki a 22.

“Na samu fasfot dina na Najeriya na farko ina da shekaru 34 lokacin da na dawo nan da zama, akwai muhawara kan ko batun dokar NYSC ya shafe ni. Da na yi tambaya kan matsayina game da NYSC, sai aka sanar da ni cewa saboda tarihin wajen zamana kuma na fi shekaru 30, an dauke mani yin bautar kasa. Sai da wannan lamari ya zo ya faru, shine iya sanina.

“Bisa ga wannan shawarar tare da jagora da taimakon wadanda nake tunanin amintattun aminai ne, an tuntubi hukumar NYSC domin ta ba da shaidarta. Daga nan na karbi takardar shaidar da ake magana. Kasancewar ban taba yin aiki a NYSC ba, ban taba ziyartar harabar ko kuma na san ayyukansu ba, ba ni da wani dalili da zan yi zargin cewa takardar shaidar ba ta gaske bace.

“Hakika, na gabatar da wannan satifiket a Majalisar Dokokin Jihar Ogun ta 2011 da kuma a shekarar 2015 don tantancewa na hukumar DSS da kuma Majalisar Dokoki ta Kasa don tantancewa. Na nemi shawarar shari’a kuma babu matsala zan iya samun takardar dauke mani zuwa NYSC.

“Na sha kunya sosai a wancan lokacin saboda ni madubin dubawa ce ga matasa. Don haka, Don haka, abin da ya faru ya watsar da darussan da na koya wa matasa na. Ina kuka a kullun tsawon watanni uku; Ban yi wa kowa ko kaina komai ba tsawon wadancan watanni. Kuka kawai nake yi, kuka, da kuka.”

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp