Home SIYASA Shugaba Buhari ya Bukaci Mambobin APC da su ci gaba da Hada...

Shugaba Buhari ya Bukaci Mambobin APC da su ci gaba da Hada Kansu Sannan su Marawa Sabon Shugabancin Jam’iyyar Baya

Shugaba Buhari ya Bukaci Mambobin APC da su ci gaba da Hada Kansu Sannan su Marawa Sabon Shugabancin Jam’iyyar Baya

 

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya shawarci Sanata Adamu Abdullahi da ya duba cancanta sama da komai wajen zabar yan takara a zaben 2023.

Shugaban kasar ya kuma bukaci mambobin APC da su ci gaba da hada kansu sannan su marawa sabon shugabancin jam’iyyar baya.

Sanata Abdullahi ne ya zama sabon shugaban jam’iyyar mai mulki a taron da aka yi a ranar Asabar, 26 ga watan Maris.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bukaci sabuwar zababbiyar uwar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) karkashin jagorancin Sanata Adamu Abdullahi da ta tabbatar da ganin cewa wadanda suka cancanta ne suka mallaki tikitin jam’iyyar a zaben 2023.

Buhari ya bukaci sabbin shugabannin da su inganta damokradiyyar cikin gida da daidaito sannan su tabbatar da ganin cewa ba’a yi cuwa-cuwa ba a zaben fidda gwanin jam’iyyar gabannin zaben 2023, rahoton Punch.

Da yake jawabi a babban taron gangamin jam’iyyar da aka yi a ranar Asabar, a Eagle Square Abuja, shugaban kasar ya kuma yi kira ga mambobin APC da su ci gaba da kasancewa a hade da karfi sannan su marawa sabon shugabancin jam’iyyar baya.

Ya ce:

“Wannan taro na zuwa ne a lokaci mai muhimmanci lokacin da muke shirin wani babban zaben. Don haka, akwai mukatar mu ci gaba da kasancewa cike da kwarin gwiwa da hadin kai domin nasarar jam’iyyarmu.

“Mun yaba da ‘yancin rike ra’ayoyi da buri daban-daban, duk da haka, dole ne kada irin wannan bambance-bambancen ya cutar da Jam’iyyar.

“Ina mai rokonku a kan duk ku ba sabon kwamitin NWC goyon baya domin inganta hadin kai da guje ma wa tunanin da zai iya haifar da rashin jituwa da rashin hadin kai.

“Ga wadanda ke takarar kujerun jam’iyyar, rashin cimma wannan kudiri naku kada ya zama dalilin da zai sa ku juyawa jam’iyyar baya.

“Ya kamata mu dauki dabi’ar yan wasan motsa jiki sannan mu dunga goyon bayan jam’iyyar a koda yaushe domin ta yi nasara.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp