Home SIYASA Shugaba Buhari ya Bukaci Mambobin APC da su ci gaba da Hada...

Shugaba Buhari ya Bukaci Mambobin APC da su ci gaba da Hada Kansu Sannan su Marawa Sabon Shugabancin Jam’iyyar Baya

Shugaba Buhari ya Bukaci Mambobin APC da su ci gaba da Hada Kansu Sannan su Marawa Sabon Shugabancin Jam’iyyar Baya

 

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya shawarci Sanata Adamu Abdullahi da ya duba cancanta sama da komai wajen zabar yan takara a zaben 2023.

Shugaban kasar ya kuma bukaci mambobin APC da su ci gaba da hada kansu sannan su marawa sabon shugabancin jam’iyyar baya.

Sanata Abdullahi ne ya zama sabon shugaban jam’iyyar mai mulki a taron da aka yi a ranar Asabar, 26 ga watan Maris.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bukaci sabuwar zababbiyar uwar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) karkashin jagorancin Sanata Adamu Abdullahi da ta tabbatar da ganin cewa wadanda suka cancanta ne suka mallaki tikitin jam’iyyar a zaben 2023.

Buhari ya bukaci sabbin shugabannin da su inganta damokradiyyar cikin gida da daidaito sannan su tabbatar da ganin cewa ba’a yi cuwa-cuwa ba a zaben fidda gwanin jam’iyyar gabannin zaben 2023, rahoton Punch.

Da yake jawabi a babban taron gangamin jam’iyyar da aka yi a ranar Asabar, a Eagle Square Abuja, shugaban kasar ya kuma yi kira ga mambobin APC da su ci gaba da kasancewa a hade da karfi sannan su marawa sabon shugabancin jam’iyyar baya.

Ya ce:

“Wannan taro na zuwa ne a lokaci mai muhimmanci lokacin da muke shirin wani babban zaben. Don haka, akwai mukatar mu ci gaba da kasancewa cike da kwarin gwiwa da hadin kai domin nasarar jam’iyyarmu.

“Mun yaba da ‘yancin rike ra’ayoyi da buri daban-daban, duk da haka, dole ne kada irin wannan bambance-bambancen ya cutar da Jam’iyyar.

“Ina mai rokonku a kan duk ku ba sabon kwamitin NWC goyon baya domin inganta hadin kai da guje ma wa tunanin da zai iya haifar da rashin jituwa da rashin hadin kai.

“Ga wadanda ke takarar kujerun jam’iyyar, rashin cimma wannan kudiri naku kada ya zama dalilin da zai sa ku juyawa jam’iyyar baya.

“Ya kamata mu dauki dabi’ar yan wasan motsa jiki sannan mu dunga goyon bayan jam’iyyar a koda yaushe domin ta yi nasara.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp