Home Taska Yanayin Tsaro: Kamfanin Jirgin Saman Azman ya Dakatar da Zirga-Zirga a Kaduna

Yanayin Tsaro: Kamfanin Jirgin Saman Azman ya Dakatar da Zirga-Zirga a Kaduna

Yanayin Tsaro: Kamfanin Jirgin Saman Azman ya Dakatar da Zirga-Zirga a Kaduna

Kamfanin jirgin saman Azman ya dakatar da zirga-zirga a jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya kwanaki kadan bayan harin da wasu ‘yan bindiga suka kai filin jirgin saman jihar inda suka kashe masu gadi da wasu ma’aikata

Kamfanin ya wallafa a shafinsa na Tuwita cewa zai dakatar da zirga-zirga a Kaduna daga ranar Litinin din da ta wuce.

Kamfanin ya ce ya dauki matakin saboda yanayi na tsaro a filin jirgin saman.

Matakin kamfanin dai ya sa matafiya sun yi cirko-cirko a filin jirgin saman na Kaduna saboda karancin jiragen da za su kai su inda za su je.

Hukumar gudanarwar kamfanin ta sanar da cewa za a dakatar da zirga-zirgar ce zuwa wani lokaci ma’ana kafin yanayin tsaro ya inganta a filin jirgin saman na Kaduna.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp