Home Taska ‘Yan Bindiga Sun Tayar da Bam a Titin Jirgin Kasa na Abuja-Kaduna

‘Yan Bindiga Sun Tayar da Bam a Titin Jirgin Kasa na Abuja-Kaduna

‘Yan Bindiga Sun Tayar da Bam a Titin Jirgin Kasa na Abuja-Kaduna

Rahotanni sun ce wasu ƴan bindiga sun tayar da bam a titin jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna da ke ɗauke da fasinja 970.

Rahotanni sun ce maharan sun yi nasarar hana jirgin tafiya, inda suka buɗe wuta.

Ɗaya daga cikin fasinjan da ke cikin jirgin ya tabbatar wa BBC da harin, inda ya ce maharan sun kwashi mutane sun tafi da su. Sannan jami’an tsaron da ke cikin jirgin sun yi musayar wuta da ƴan bindigar.

Ya ce sun kashe mutum guda. “Mun ji ƙarar harbe harbe, muna cikin tashin hankali,” in ji shi.

Wani ma’aikacin tashar jirgin a Rigasa ya shaida wa BBC cewa “jirgin ya kamata ya iso misalin ƙarfe 8:20 amma har yanzu ba labari.”

Hukumomin sufurin jiragen ƙasa ta Najeriya da hukumomin gwamnatin Kaduna ba su tabbatar da al’amarin ba.

Karin bayani na tafe….

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp