Home SIYASA Abubuwan da Zan Cimma Idan na Zama Shugaban Kasa a 2023 –...

Abubuwan da Zan Cimma Idan na Zama Shugaban Kasa a 2023 – Gwamna Wike

Abubuwan da Zan Cimma Idan na Zama Shugaban Kasa a 2023 – Gwamna Wike

 

Gwamnan jihar Ribas, ya bayyana abubuwan da yake so ya cimma idan ya zama shugaban kasa a zaben 2023.

Ya bayyana cewa, yana da yakinin dawo da zaman lafiya kasar nan matukar aka zabe shi domin ya gaje Buhari.

Gwamnan ya kuma bayyana cewa, Najeriya na bukatar shugaba kamarsa domin ciyar da kasar gaba da magance matsaloli.

Benue- Gwamna Nyesom Wike na jihar Ribas ya ce da yardar Allah zai lashe zaben shugaban kasa na 2023 da aka sa a gaba.

Wike ya bayyana hakan ne a yayin wani taron tuntuba da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP reshen Benue a gidan gwamnati da ke Makurdi a ranar Lahadi.

Hakan na zuwa ne kwana guda bayan da gwamnan na jam’iyyar PDP ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a karon farko a zabe mai zuwa, kamar yadda ya tada a Twitter.

Wike ya ci gaba da cewa, tare da jama’a za su aiwatar da wani tsari na hadin gwiwa don dawo da zaman lafiya da tsaro a ‘yan Najeriya.

Ya kuma sha alwashin magance matsalar rashin tsaro kwata-kwata a kasar matukar ya zama shugaba a 2023.

Ba Wike kadai bane dan jam’iyyar PDP da ya bayyana aniyar tsayawa takara a zaben mai zuwa ba.

Da yake amsa tambaya kan abin da zai yi na daban ga kasar nan idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa, Gwamna Wike ya sha alwashin magance matsalar rashin tsaro da ke kara kamari a kasar.

Gwamnan wanda ya yi Allah wadai da harin ta’addancin da aka kai a filin jirgin sama na Kaduna a karshen mako, ya ce ‘yan Najeriya na bukatar shugaba mai daukar matakin gaggawa da zai magance matsalar rashin tsaro a kasar.

Da yake nasa jawabin, Wike ya bayar da tabbacin cewa idan aka zabe shi, gwamnatinsa za ta samar da doka da oda domin a samu karin hannayen jarin kasashen waje kai tsaye zuwa kasar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp