Home SIYASA Shugaba Buhari ya ta ya Tinubu Murnar Cika Shekaru 70 da Haihuwa

Shugaba Buhari ya ta ya Tinubu Murnar Cika Shekaru 70 da Haihuwa

Shugaba Buhari ya ta ya Tinubu Murnar Cika Shekaru 70 da Haihuwa

 

Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, jigon jam’iyyar APC kuma dan takarar shugaban kasa a zaben 2023, zai cika shekaru 70 a ranar Talata, 29 ga Maris.

Gabanin bikin zagayowar ranar haihuwarsa, shugaba Buhari Buhari ya fitar da sanarwar taya murna ga tsohon gwamnan jihar Legas.

Shugaban ya jinjinawa jajircewa, juriya, rashin nuna son kai da martabar Tinubu wajen fifita jin dadin al’umma da hadin kan al’umma sama da son rai.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bi sahun ‘ya’yan APC da shuwagabanninta wajen taya jagoran jam’iyyar na kasa kuma tsohon gwamnan jihar Legas, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu murnar cika shekaru 70 da haihuwa a ranar 29 ga Maris, 2022.

Shugaban kasar, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin ta hannun mai magana da yawunsa, Femi Adesina, ya tabbatar da irin gudunmawar da jigon na APC ke bayarwa ga ci gaban siyasa, tattalin arziki da zamantakewar kasar nan.

Daily Trust ta rahoto cewa, Buhari ya kuma yaba da jajircewarsa, juriyarsa, rashin nuna son kai da martabarsa a ko da yaushe yana fifita hadin kan al’umma sama da son kai.

Hakazalika, tare da samun goyon baya da hangen nesan Najeriya mai girma ta hanyar zuba jari ga mutane, hukumomi da gwamnatoci, ba tare da tunanin kabilanci ko akida ba.

Ya kuma yi addu’ar Allah ya karawa Asiwaju Tinubu, Jagaban Masarautar Borgu karfi da lafiya da hikima domin ya ci gaba da yi wa kasa hidima da kuma bil’adama baki daya.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp