Home Labarai Jami’an Tsaron Najeriya Sun Nuna Jajircewa, Sun Cancanci Yabo – Lai Mohammed

Jami’an Tsaron Najeriya Sun Nuna Jajircewa, Sun Cancanci Yabo – Lai Mohammed

Jami’an Tsaron Najeriya Sun Nuna Jajircewa, Sun Cancanci Yabo – Lai Mohammed

Gwamnatin tarayya tace kowace rana Najeriya na ƙara samun aminci da zaman lafiya ta kowane ɓangare.

Ministan yaɗa labarai da Al’adu, Alhaji Lai Mohammed, ya ce jami’an tsaron Najeriya sun nuna jajircewa, sun cancanci yabo .

Ministan ya yi bayanin yadda gwamnatin tarayya ta taimaka wa jami’an tsaro da kayan aiki har ake samun nasara.

Abuja- Gwamnatin tarayya tace Najeriya na samun zaman lafiya da aminci kowace rana tare da nasarori a yaƙin da take da Boko Haram/ISWAP, yan bindiga da sauran ayyukan ta’addanci.

Ministan yaɗa labarai da Al’adu, Alhaji Lai Muhammed, ne ya faɗi haka a wurin taron manema labarai a Abuja ranar Litinin, kamar yadda The Nation ta rahoto.

Yace dakarun tsaro a Najeriya sun zafafa yaƙi da yan bindiga kuma suka jefa su cikin halin gudun ɓuya yayin da kullum ake ƙara tarwatsa sansanonin su.

A jawabinsa ya ce:

“Ina alfahari da jami’an tsaron mu maza da mata dake cin ɗamara, duk da taɓarɓarewar ƙalubalen tsaro, ba su karaya ba kuma sun jajirce.”

“A dai-dai lokacin da suka tarwatsa yan ta’addaa sansanonin su, wasu dubbanni tare da iyalansu na miƙa wuya tare da aje makamai.”

“Hukumomin tsaro sun tsaya da digadigan su ne bisa jagorancin da shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ke samar musu da kuma sadaukarwan jami’an tsaro da shugabannin su.”

Yadda FG ta samar da kayan aiki

Muhammed ya bayyana cewa sama da sojoji 1,500 aka ɗauka aiki a rundunar sojin ruwa cikin shekarar nan yayin da sojojin sama (NAF) suka karɓi sabbin jiragen yaƙin Super Tucano 12 da JF-17 Thunder Fighter guda uku.

Ya ce dakarun sojin sun yi amfani da jiragen wajen luguden wuta ta sama, taimakawa sojin ƙasa, da kuma lalata sansanonin yan bindiga da makamansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp