Home Taska An Harbi Tsohon Mataimakin Gwamnan Zamfara, Ibrahim Wakkala a Harin Jirgin Kasar...

An Harbi Tsohon Mataimakin Gwamnan Zamfara, Ibrahim Wakkala a Harin Jirgin Kasar Abuja-Kaduna

An Harbi Tsohon Mataimakin Gwamnan Zamfara, Ibrahim Wakkala a Harin Jirgin Kasar Abuja-Kaduna

Tsohon mataimakin gwamnan Zamfara, Ibrahim Wakkala, na a cikin jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja da aka kaiwa hari a ranar Litinin.

Wakkala ya samu rauni ta sanadiyar harbin bindiga bayan tawagar tsaro sun ceto shi daga hannun yan bindigar da suka yi garkuwa da shi a yayin harin.

Yana a hanyarsa ta dawowa ne daga babban taron gangamin APC da aka yi a karshen mako.

Kaduna- Tsohon mataimakin gwamnan jihar Zamfara, Ibrahim Wakkala, ya ji rauni daga harbin bindiga a harin ta’addanci da aka kai kan jirgin kasar Kaduna zuwa Abuja a ranar Litinin, 28 ga watan Maris.

Yan bindiga sun far ma jirgin kasan da ke dauke da daruruwan fasinjoji a tsakanin Katari da Rijana a jihar Kaduna.

Wani hadimin tsohon mataimakin gwamnan ya fada ma talbijin din Channel cewa an harbi Mista Wakkala ne wanda ke dawowa daga babban taron APC da aka yi a ranar Asabar a yayin musayar wuta tsakanin yan ta’addan da sojoji.

Ya kuma ce an kwashe shi zuwa wani asibitin sojoji da ke Kaduna domin jinya.

Kakakin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a jihar Zamfara, Yusuf Idris ya kuma tabbatar da lamarin ga gidan talbijin din.

Idris ya ce da farko yan bindiga sun sace tsohon mataimakin gwamnan a yayin harin amma sai tawagar hadin gwiwa ta DSS da sojoji suka yi nasarar ceto shi.

“Da farko sun sace shi amma sai DSS da sojoji suka ceto shi, a cikin haka ne ya ji rauni ta sanadiyar harbin bindiga a kafarsa.

“Ya daidaita sosai a yanzu, yana samun kulawar likitoci a asibitin jihar Kaduna.”

Daily Trust takuma nakalto Idris na kara cewa:

“Yana samun sauki sosai. Yana amsa kiraye-kirayen waya a gadonsa na asibiti. Na yi magana da shi kuma wasu mutane da dama ma sun yi. Babu wani abun tashin hankali.”

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp