Home Taska Yajin Aikin ASUU: Za mu Mayar da Titunan Abuja Ajujuwanmu Har Zuwa...

Yajin Aikin ASUU: Za mu Mayar da Titunan Abuja Ajujuwanmu Har Zuwa Lokacin da aka Bude Makarantu – NANS 

Yajin Aikin ASUU: Za mu Mayar da Titunan Abuja Ajujuwanmu Har Zuwa Lokacin da aka Bude Makarantu – NANS 

Daliban Najeriya karkashin kungiyar NANS za su cigaba da yin zanga-zanga a titunan Abuja kan yajin aikin da ASUU ke yi.

Sunday Asefon, shugaban kungiyar daliban, NANS, ya ce ba za su dena zanga-zangar ba har sai an bude dukkan jami’o’in da ke kasar.

A cewarsa, tunda an rufe ajujuwansu na makaranta, za su mayar da titunan Abuja ajujuwansu har zuwa lokacin da aka bude makarantun.

FCT, Abuja – Kungiyar Daliban Najeriya, NANS, a ranar Litinin ta cigaba da zanga-zangar ta na neman ganin an kawo karshen yakin aikin da kungiyar malaman jami’o’i, ASUU, ke yi.

Da ya ke magana a yayin zanga-zangar a Abuja, shugaban NANS na kasa, Sunday Asefon, ya ce daliban a shirye suke su fito su mamaye manyan titunan Abuja, rahoton The Punch.

Mun gaji, ba mu damu da abin da zai faru ba sakamakon zanga-zangar, Shugaban NANS

Ya kara da cewa daliban sun gaji kuma ba za su fasa abin da suka fara ba har zai an bude dukkan jami’o’i a kasar.

Asefon ya ce:

“Tunda sun kore mu daga ajujuwan mu za mu mayar da titunan Abuja dakunan karatun mu.

“Wannan ba wasan yara bane, da gaske muke yi a yanzu. Sakon mu mai sauki ne: A bude mana jami’o’in mu. Mun tabbatar idan ba a janye yakin aikin nan ba, Daliban Najeriya ba za su bar tituna ba.

“Za mu koma titunan ba tare da damuwa da abin da zai faru ba. Mutanen Abuja su sani cewa za mu mamaye manyan titunan a matsayin wani mataki na ganin an bude makarantun mu.”

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp