Home Taska Yajin Aikin ASUU: Za mu Mayar da Titunan Abuja Ajujuwanmu Har Zuwa...

Yajin Aikin ASUU: Za mu Mayar da Titunan Abuja Ajujuwanmu Har Zuwa Lokacin da aka Bude Makarantu – NANS 

Yajin Aikin ASUU: Za mu Mayar da Titunan Abuja Ajujuwanmu Har Zuwa Lokacin da aka Bude Makarantu – NANS 

Daliban Najeriya karkashin kungiyar NANS za su cigaba da yin zanga-zanga a titunan Abuja kan yajin aikin da ASUU ke yi.

Sunday Asefon, shugaban kungiyar daliban, NANS, ya ce ba za su dena zanga-zangar ba har sai an bude dukkan jami’o’in da ke kasar.

A cewarsa, tunda an rufe ajujuwansu na makaranta, za su mayar da titunan Abuja ajujuwansu har zuwa lokacin da aka bude makarantun.

FCT, Abuja – Kungiyar Daliban Najeriya, NANS, a ranar Litinin ta cigaba da zanga-zangar ta na neman ganin an kawo karshen yakin aikin da kungiyar malaman jami’o’i, ASUU, ke yi.

Da ya ke magana a yayin zanga-zangar a Abuja, shugaban NANS na kasa, Sunday Asefon, ya ce daliban a shirye suke su fito su mamaye manyan titunan Abuja, rahoton The Punch.

Mun gaji, ba mu damu da abin da zai faru ba sakamakon zanga-zangar, Shugaban NANS

Ya kara da cewa daliban sun gaji kuma ba za su fasa abin da suka fara ba har zai an bude dukkan jami’o’i a kasar.

Asefon ya ce:

“Tunda sun kore mu daga ajujuwan mu za mu mayar da titunan Abuja dakunan karatun mu.

“Wannan ba wasan yara bane, da gaske muke yi a yanzu. Sakon mu mai sauki ne: A bude mana jami’o’in mu. Mun tabbatar idan ba a janye yakin aikin nan ba, Daliban Najeriya ba za su bar tituna ba.

“Za mu koma titunan ba tare da damuwa da abin da zai faru ba. Mutanen Abuja su sani cewa za mu mamaye manyan titunan a matsayin wani mataki na ganin an bude makarantun mu.”

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp