Home Taska Yajin Aikin ASUU: Za mu Mayar da Titunan Abuja Ajujuwanmu Har Zuwa...

Yajin Aikin ASUU: Za mu Mayar da Titunan Abuja Ajujuwanmu Har Zuwa Lokacin da aka Bude Makarantu – NANS 

Yajin Aikin ASUU: Za mu Mayar da Titunan Abuja Ajujuwanmu Har Zuwa Lokacin da aka Bude Makarantu – NANS 

Daliban Najeriya karkashin kungiyar NANS za su cigaba da yin zanga-zanga a titunan Abuja kan yajin aikin da ASUU ke yi.

Sunday Asefon, shugaban kungiyar daliban, NANS, ya ce ba za su dena zanga-zangar ba har sai an bude dukkan jami’o’in da ke kasar.

A cewarsa, tunda an rufe ajujuwansu na makaranta, za su mayar da titunan Abuja ajujuwansu har zuwa lokacin da aka bude makarantun.

FCT, Abuja – Kungiyar Daliban Najeriya, NANS, a ranar Litinin ta cigaba da zanga-zangar ta na neman ganin an kawo karshen yakin aikin da kungiyar malaman jami’o’i, ASUU, ke yi.

Da ya ke magana a yayin zanga-zangar a Abuja, shugaban NANS na kasa, Sunday Asefon, ya ce daliban a shirye suke su fito su mamaye manyan titunan Abuja, rahoton The Punch.

Mun gaji, ba mu damu da abin da zai faru ba sakamakon zanga-zangar, Shugaban NANS

Ya kara da cewa daliban sun gaji kuma ba za su fasa abin da suka fara ba har zai an bude dukkan jami’o’i a kasar.

Asefon ya ce:

“Tunda sun kore mu daga ajujuwan mu za mu mayar da titunan Abuja dakunan karatun mu.

“Wannan ba wasan yara bane, da gaske muke yi a yanzu. Sakon mu mai sauki ne: A bude mana jami’o’in mu. Mun tabbatar idan ba a janye yakin aikin nan ba, Daliban Najeriya ba za su bar tituna ba.

“Za mu koma titunan ba tare da damuwa da abin da zai faru ba. Mutanen Abuja su sani cewa za mu mamaye manyan titunan a matsayin wani mataki na ganin an bude makarantun mu.”

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp