Home Taska Shugaban NITDA ya Buɗe Katafaren Ɗakin Gwaje-Gwajen Ƙirƙira na Ƙasa

Shugaban NITDA ya Buɗe Katafaren Ɗakin Gwaje-Gwajen Ƙirƙira na Ƙasa

Kashifu Open

Shugaban NITDA ya Buɗe Katafaren Ɗakin Gwaje-Gwajen Ƙirƙira na Ƙasa

Mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamami ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), a yau ya buɗe wani katafaren ɗakin zamani na gwaje-gwajen ƙere-ƙeren kayayyakin fasahar sadarwar zamani, wanda su ka samar a cibiyar ƙasa ta nazari da ƙere-ƙeren na’urori masu ɗabi’u irin na bil’adama, “National Centre for Artificial Intelligence and Robotics (NCAIR), da ke Abuja.

Testing Room

Samar da ɗakin gwaje-gwajen ƙirƙirar, wani ƙoƙari ne na cika umarnin da mai girma shugaban ƙasa Malam Muhammadu Buhari (GCFR), ya ba wa mai girma ministan sadarwa da tattalin arziƙin fasahar zamani, Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, (FNCS, FBCS, FIIM), na sabunta Nageriya tayadda za ta jagoranci Duniya wajen harkar ƙere-ƙeren kayayyakin fasahar sadarwar zamani kan kasuwanci.

Katafaren ɗakin gwaje-gwajen ƙirƙirar, ɗaki ne na zamani irin wanda ake da shi a ƙasashen duniya da su ka cigaba kan harkar fasahar zamani. An kuma wadata shi da dukkan wasu nau’ikan na’urori waɗanda masu nazari da baiwar kirkira su ke buƙata wajen samar da wata ƙirƙira ta fasahar sadarwar zamani ko gwada wani tunani da su ka yi domin tabbata.

Daɗi da ƙari, an kuma yi wa ɗakin rijista da gidauniyar ɗakin gwajin ƙirƙira ta duniya wanda ƙungiya ce ta duniya da ke samarwa, gami da ba da gudunmawa wajen haɓakawa gami da bunƙasa sabis ɗin ire-iren ɗakin a duk duniya.

Haka zalika, daga wannan rana ɗakin zai cigaba da kasancewa a buɗe ga duk ƴan Nageriya masu baiwa da fasahar ƙirƙira domin su samar da ƙere-ƙeren da su ka yi tunani a zahiri tayadda za su amfana su amfani ƙasa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp