Home Taska Lambobin Yabo ga Shugaban NITDA

Lambobin Yabo ga Shugaban NITDA

Kashifu pantami

Lambobin Yabo ga Shugaban NITDA

Hoto Na Farko:- Ƙungiyar Injiniyoyin lantarki, Institute of Electrical and Electronic Engineers (IEEE), ne su ka karrama mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), da lambar yabo, yau a wurin taronsu na shekara-shekara karo na huɗu domin yabawa haɗi da jinjina kan gudunmawar da ya ke ba su.

Mai girma ministan sadarwa da tattalin arziƙin fasahar zamani, Shaik, Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, (FNCS, FBCS, FIIM), da ya miƙa masa lambar yabon, ya kasance babban baƙo mai gabatar da jawabi a wurin taron a bana, (2022).

Hoto Na Biyu: Ƙungiyar Jakadun jam’iyyar (APC), dangane da shugabanci nagari, “APC Ambassadors for Good Governance”, ita ce ta karrama mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), da lambar yabo ta jinjina a gare shi akan ƙoƙarin da ya ke yi wajen cimma buri da manufofin gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari (GCFR), kan tattalin arziƙin zamani.

Shugaban riƙo na sashen tsare-tsare na hukumar ta (NITDA), Dakta Aristotle Onumo, shi ne ya karɓi lambar yabon a madadinsa, jiya, a wurin babban taron ƙungiyar na ƙaddamarwa da rantsar da shugabanninta na Jihohi (36).

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp