Home Taska Lambobin Yabo ga Shugaban NITDA

Lambobin Yabo ga Shugaban NITDA

Kashifu pantami

Lambobin Yabo ga Shugaban NITDA

Hoto Na Farko:- Ƙungiyar Injiniyoyin lantarki, Institute of Electrical and Electronic Engineers (IEEE), ne su ka karrama mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), da lambar yabo, yau a wurin taronsu na shekara-shekara karo na huɗu domin yabawa haɗi da jinjina kan gudunmawar da ya ke ba su.

Mai girma ministan sadarwa da tattalin arziƙin fasahar zamani, Shaik, Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, (FNCS, FBCS, FIIM), da ya miƙa masa lambar yabon, ya kasance babban baƙo mai gabatar da jawabi a wurin taron a bana, (2022).

Hoto Na Biyu: Ƙungiyar Jakadun jam’iyyar (APC), dangane da shugabanci nagari, “APC Ambassadors for Good Governance”, ita ce ta karrama mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), da lambar yabo ta jinjina a gare shi akan ƙoƙarin da ya ke yi wajen cimma buri da manufofin gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari (GCFR), kan tattalin arziƙin zamani.

Shugaban riƙo na sashen tsare-tsare na hukumar ta (NITDA), Dakta Aristotle Onumo, shi ne ya karɓi lambar yabon a madadinsa, jiya, a wurin babban taron ƙungiyar na ƙaddamarwa da rantsar da shugabanninta na Jihohi (36).

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp