Home Taska Lambobin Yabo ga Shugaban NITDA

Lambobin Yabo ga Shugaban NITDA

Kashifu pantami

Lambobin Yabo ga Shugaban NITDA

Hoto Na Farko:- Ƙungiyar Injiniyoyin lantarki, Institute of Electrical and Electronic Engineers (IEEE), ne su ka karrama mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), da lambar yabo, yau a wurin taronsu na shekara-shekara karo na huɗu domin yabawa haɗi da jinjina kan gudunmawar da ya ke ba su.

Mai girma ministan sadarwa da tattalin arziƙin fasahar zamani, Shaik, Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, (FNCS, FBCS, FIIM), da ya miƙa masa lambar yabon, ya kasance babban baƙo mai gabatar da jawabi a wurin taron a bana, (2022).

Hoto Na Biyu: Ƙungiyar Jakadun jam’iyyar (APC), dangane da shugabanci nagari, “APC Ambassadors for Good Governance”, ita ce ta karrama mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), da lambar yabo ta jinjina a gare shi akan ƙoƙarin da ya ke yi wajen cimma buri da manufofin gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari (GCFR), kan tattalin arziƙin zamani.

Shugaban riƙo na sashen tsare-tsare na hukumar ta (NITDA), Dakta Aristotle Onumo, shi ne ya karɓi lambar yabon a madadinsa, jiya, a wurin babban taron ƙungiyar na ƙaddamarwa da rantsar da shugabanninta na Jihohi (36).

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Jami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga PantamiGazawar Demarketing: Yadda Sukar Rarara Mai Cike da Kiyayya ga Pantami Ya Rushe Daga Yushau A. ShuaibƘungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin AikiDakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da suƳan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari'a da ke Jihar Katsina
X whatsapp