Home Labarai Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Tabbatar da Mutum 7 Sakamakon Harin...

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Tabbatar da Mutum 7 Sakamakon Harin ‘Yan Bindiga A Jihar

A kalla mutum 7 ne suka mutu sakamakon harin ‘Yan bindiga a kauyen Kurfi dake karamar hukumar Takai a jihar Kano.

Mazauna yankin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi awon gaba da Dagacin Garin tare da raunata Mutum 3 a yayin harin.

Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya bayyanawa manema labarai cewa tuni hukumar ‘Yan sandan jihar ta tura jami’an ta domin bin sahun ‘yan bindigar.

Wani shaidar gani da Ido Sale Hussaini ya bayyanawa PRNigeria cewa, ‘yan bindigar sun kaddamar da harin ranar Asabar daakrfe 11 dare, inda kai tsayi suka durfafi gidan mai Gari.

Ya bayyana sunan Dagacin Kauyen da Abdul-hayatu Ilu, inda yace guda cikin wadanda aka kashe makoci ne ga mai rike da sauatar gargajiyar.

‘Yan bindigar kuma suna halaka mutum 5 garin Tudun Makama dake makotaka da kauyen, bayan da AL’umma suka bi bayan ‘yan bindigar.

Ya kuma bayyana sunayen wadanda ‘yan bindigar suka halaka da suka hadar da Tasi’u Birniyo, Ali Yahaya, Hashimmu Amo, Sadiq hussaini, Ahmadu danlanbu, bala Audu da kuma Shu’aibu Agwar-maji.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp