Home Labarai Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Tabbatar da Mutum 7 Sakamakon Harin...

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Tabbatar da Mutum 7 Sakamakon Harin ‘Yan Bindiga A Jihar

A kalla mutum 7 ne suka mutu sakamakon harin ‘Yan bindiga a kauyen Kurfi dake karamar hukumar Takai a jihar Kano.

Mazauna yankin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi awon gaba da Dagacin Garin tare da raunata Mutum 3 a yayin harin.

Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya bayyanawa manema labarai cewa tuni hukumar ‘Yan sandan jihar ta tura jami’an ta domin bin sahun ‘yan bindigar.

Wani shaidar gani da Ido Sale Hussaini ya bayyanawa PRNigeria cewa, ‘yan bindigar sun kaddamar da harin ranar Asabar daakrfe 11 dare, inda kai tsayi suka durfafi gidan mai Gari.

Ya bayyana sunan Dagacin Kauyen da Abdul-hayatu Ilu, inda yace guda cikin wadanda aka kashe makoci ne ga mai rike da sauatar gargajiyar.

‘Yan bindigar kuma suna halaka mutum 5 garin Tudun Makama dake makotaka da kauyen, bayan da AL’umma suka bi bayan ‘yan bindigar.

Ya kuma bayyana sunayen wadanda ‘yan bindigar suka halaka da suka hadar da Tasi’u Birniyo, Ali Yahaya, Hashimmu Amo, Sadiq hussaini, Ahmadu danlanbu, bala Audu da kuma Shu’aibu Agwar-maji.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp