Home Labarai Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Tabbatar da Mutum 7 Sakamakon Harin...

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Tabbatar da Mutum 7 Sakamakon Harin ‘Yan Bindiga A Jihar

A kalla mutum 7 ne suka mutu sakamakon harin ‘Yan bindiga a kauyen Kurfi dake karamar hukumar Takai a jihar Kano.

Mazauna yankin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi awon gaba da Dagacin Garin tare da raunata Mutum 3 a yayin harin.

Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya bayyanawa manema labarai cewa tuni hukumar ‘Yan sandan jihar ta tura jami’an ta domin bin sahun ‘yan bindigar.

Wani shaidar gani da Ido Sale Hussaini ya bayyanawa PRNigeria cewa, ‘yan bindigar sun kaddamar da harin ranar Asabar daakrfe 11 dare, inda kai tsayi suka durfafi gidan mai Gari.

Ya bayyana sunan Dagacin Kauyen da Abdul-hayatu Ilu, inda yace guda cikin wadanda aka kashe makoci ne ga mai rike da sauatar gargajiyar.

‘Yan bindigar kuma suna halaka mutum 5 garin Tudun Makama dake makotaka da kauyen, bayan da AL’umma suka bi bayan ‘yan bindigar.

Ya kuma bayyana sunayen wadanda ‘yan bindigar suka halaka da suka hadar da Tasi’u Birniyo, Ali Yahaya, Hashimmu Amo, Sadiq hussaini, Ahmadu danlanbu, bala Audu da kuma Shu’aibu Agwar-maji.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp