Home Labarai Alkalin Alkalan Nijeriya Yayi Murabus

Alkalin Alkalan Nijeriya Yayi Murabus

Alkalin Alkalan Nijeriya (CJN) mai shari’a Muhammad Tanko yayi murabus daga mukamin sa na babban mai shari’a a kotun koli.

Rahotannin sun bayyana cewa ya yi murabus din ne sakamakon rashin lafiya  da yake fama da ita.

Ana sa rana daga na zuwa ko wanne lokaci za’a maye gurbin sa da mai shari’a olukayode Ariwoola , wannan da ke matsayin mafi girma bayan mai shari’a Mary Odili wadda tayi ritaya  12 ga watan mayun bayan ta cika shekaru 70 a matsayin mukaddashi.

An dai hafi Mai shari’a Muhammad a garin Doguwa, dake karamar hukumar Gaide ta jihar Bauchi a ranar 31, Disamban 1953.

Ya halarci makaranatr Firamare ta Giade daga 1961 zuwa 1968, inda ya tafi zuwa sakandire ta Azare a shekarar 1969 zuwa 1973, daga bisani  ya zuwa makarantar Abdullahi Bayero University College, kano inda yayi karatun share fagen shiga jami’a na IJMB daga shekarar 1975 zuwa 1976, bayan ya sami nasarar ne ya sammi gurbin karatu a jami’ar Ahmadu Bello dake Zaria daga shekara 1976 zuwa 1980, ya kuma halarci kwalejin  koyan aikin shari’a daga shekarar 1980 zuwa 1981.

Domin Karin karatu ya koma zuwa jami’ar Ahmadu Bello dake Zari’a, inda ya sake samun digiri na 2 a fannin shari’a (LLM) a wani tsari na wucin gadi daga shekarar1982 zuwa 1984.

Saboda sake samun gogewa a fannin ya dora dai a jami’ar ta Ahmadu Bello domin samu digirin na 3 (PhD) a fanin shari’a duk dai a tsarin wucin gadi.

Daga bisani shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya rantsar da shi a matsayin Alkalin Alkalan kasar a watan Janairun 2019, bayan dakatar da mai shari’a Walter Onnoghen.

Bisa doka dai dukkan babban Alkalin kotun koli a Nijeriya wajibi ne yayi murabus da zarar ya kai shekara 70 a duniya.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp