Home Labarai Alkalin Alkalan Nijeriya Yayi Murabus

Alkalin Alkalan Nijeriya Yayi Murabus

Alkalin Alkalan Nijeriya (CJN) mai shari’a Muhammad Tanko yayi murabus daga mukamin sa na babban mai shari’a a kotun koli.

Rahotannin sun bayyana cewa ya yi murabus din ne sakamakon rashin lafiya  da yake fama da ita.

Ana sa rana daga na zuwa ko wanne lokaci za’a maye gurbin sa da mai shari’a olukayode Ariwoola , wannan da ke matsayin mafi girma bayan mai shari’a Mary Odili wadda tayi ritaya  12 ga watan mayun bayan ta cika shekaru 70 a matsayin mukaddashi.

An dai hafi Mai shari’a Muhammad a garin Doguwa, dake karamar hukumar Gaide ta jihar Bauchi a ranar 31, Disamban 1953.

Ya halarci makaranatr Firamare ta Giade daga 1961 zuwa 1968, inda ya tafi zuwa sakandire ta Azare a shekarar 1969 zuwa 1973, daga bisani  ya zuwa makarantar Abdullahi Bayero University College, kano inda yayi karatun share fagen shiga jami’a na IJMB daga shekarar 1975 zuwa 1976, bayan ya sami nasarar ne ya sammi gurbin karatu a jami’ar Ahmadu Bello dake Zaria daga shekara 1976 zuwa 1980, ya kuma halarci kwalejin  koyan aikin shari’a daga shekarar 1980 zuwa 1981.

Domin Karin karatu ya koma zuwa jami’ar Ahmadu Bello dake Zari’a, inda ya sake samun digiri na 2 a fannin shari’a (LLM) a wani tsari na wucin gadi daga shekarar1982 zuwa 1984.

Saboda sake samun gogewa a fannin ya dora dai a jami’ar ta Ahmadu Bello domin samu digirin na 3 (PhD) a fanin shari’a duk dai a tsarin wucin gadi.

Daga bisani shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya rantsar da shi a matsayin Alkalin Alkalan kasar a watan Janairun 2019, bayan dakatar da mai shari’a Walter Onnoghen.

Bisa doka dai dukkan babban Alkalin kotun koli a Nijeriya wajibi ne yayi murabus da zarar ya kai shekara 70 a duniya.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp