Home Labarai ‘Yan Bindiga Sunyi garkuwa Da DPO A Jihar Kaduna

‘Yan Bindiga Sunyi garkuwa Da DPO A Jihar Kaduna

‘Yan bindiga masu garkuwa da mutane sun kama sabon baturen ‘yan sanda da aka tura karamar hukumar birnin Gwari dake jihar kaduna.

Anyi garkuwa da baturen ‘yan sandan ne akan babbar hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari da misalin karfe 9 na safiyar ranar litinin a yayin da yake kokarin zuwa inda aka turashi domin kama aiki.

Wata majiya ta sai dawa PRNigeria cewa baturen ‘yan Sandan (DPO) na kan hanyar sa zuwa birnin Gwari masu garkuwar suka kama shi, sai kawo yanzu ba’a tabbatar da ko yayi tafiya shi kadai bane ko akasin haka.

Kawo yanzu dai hukumar ‘yan sandan jihar na tattara bayanai domin fidda sanarwa a hukumance, kamar yadda kakakin Rundunar ‘yan sandan jihar ta Kaduna Muhammad Jalige ya bayyana.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp