Home Labarai Gwamnan Jihar Osun Adegboyega Oyetola ya Mika Ta’aziyyar Sa Bisa Rasuwar Imam...

Gwamnan Jihar Osun Adegboyega Oyetola ya Mika Ta’aziyyar Sa Bisa Rasuwar Imam Agaka

Gwamnan jihar Osun Adegboyega Oyetola, ya mika sakon ta’aziyyar sa ga babban mai tace labarai na Jaridar PRNigeria da Economic Confidential Malam Yusha’u shu’aib, bisa rasuwar mahaifin sa, Imam Abdulhameed Shuaib Agaka.

Wannan dai na cikin wata wasikar mai dauke da sa hannun Gwamnan, wadda ke bayyana Imam Agaka matsayin wata taska da Al’umma ke kwasar romon ilimi, baya ga sadaukar da kai wajen yiwa kasa da Al’ummar ta aikin daya kama, wadda kuma hidimar zata zama abin koyi ga masu tasowa anan gaba.

Shahararren malamin ya rasu ne kwanan nan kuma tuni  aka yi masa sutura (binne shi) bisa tanadin addinin musulunci, a garin Ilori dake jihar kwara.

Ta cikin wasikar da mai Magana da yawun sa Isma’il Omipidan, ya kawo kafa da kafa Shalkwatar jaridar ta PRNigeria dake Birnin Abuja, Gwamnan ya bukaci Malam Yusha’u ya dauki danga tare da koyi da irin rayuwar da mahaifin sa yayi kasancewar sa fitaccen mai Ilimi wanda ke amfani da ilimin yadda ya kamata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp