Home Labarai Gwamnan Jihar Osun Adegboyega Oyetola ya Mika Ta’aziyyar Sa Bisa Rasuwar Imam...

Gwamnan Jihar Osun Adegboyega Oyetola ya Mika Ta’aziyyar Sa Bisa Rasuwar Imam Agaka

Gwamnan jihar Osun Adegboyega Oyetola, ya mika sakon ta’aziyyar sa ga babban mai tace labarai na Jaridar PRNigeria da Economic Confidential Malam Yusha’u shu’aib, bisa rasuwar mahaifin sa, Imam Abdulhameed Shuaib Agaka.

Wannan dai na cikin wata wasikar mai dauke da sa hannun Gwamnan, wadda ke bayyana Imam Agaka matsayin wata taska da Al’umma ke kwasar romon ilimi, baya ga sadaukar da kai wajen yiwa kasa da Al’ummar ta aikin daya kama, wadda kuma hidimar zata zama abin koyi ga masu tasowa anan gaba.

Shahararren malamin ya rasu ne kwanan nan kuma tuni  aka yi masa sutura (binne shi) bisa tanadin addinin musulunci, a garin Ilori dake jihar kwara.

Ta cikin wasikar da mai Magana da yawun sa Isma’il Omipidan, ya kawo kafa da kafa Shalkwatar jaridar ta PRNigeria dake Birnin Abuja, Gwamnan ya bukaci Malam Yusha’u ya dauki danga tare da koyi da irin rayuwar da mahaifin sa yayi kasancewar sa fitaccen mai Ilimi wanda ke amfani da ilimin yadda ya kamata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp