Home Labarai Gwamnan Jihar Osun Adegboyega Oyetola ya Mika Ta’aziyyar Sa Bisa Rasuwar Imam...

Gwamnan Jihar Osun Adegboyega Oyetola ya Mika Ta’aziyyar Sa Bisa Rasuwar Imam Agaka

Gwamnan jihar Osun Adegboyega Oyetola, ya mika sakon ta’aziyyar sa ga babban mai tace labarai na Jaridar PRNigeria da Economic Confidential Malam Yusha’u shu’aib, bisa rasuwar mahaifin sa, Imam Abdulhameed Shuaib Agaka.

Wannan dai na cikin wata wasikar mai dauke da sa hannun Gwamnan, wadda ke bayyana Imam Agaka matsayin wata taska da Al’umma ke kwasar romon ilimi, baya ga sadaukar da kai wajen yiwa kasa da Al’ummar ta aikin daya kama, wadda kuma hidimar zata zama abin koyi ga masu tasowa anan gaba.

Shahararren malamin ya rasu ne kwanan nan kuma tuni  aka yi masa sutura (binne shi) bisa tanadin addinin musulunci, a garin Ilori dake jihar kwara.

Ta cikin wasikar da mai Magana da yawun sa Isma’il Omipidan, ya kawo kafa da kafa Shalkwatar jaridar ta PRNigeria dake Birnin Abuja, Gwamnan ya bukaci Malam Yusha’u ya dauki danga tare da koyi da irin rayuwar da mahaifin sa yayi kasancewar sa fitaccen mai Ilimi wanda ke amfani da ilimin yadda ya kamata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp