Home Labarai Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kudirin Ta Na Kare Fararen Hular...

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kudirin Ta Na Kare Fararen Hular Kasar

Rundunar sojin Nijeriya ta tabbatar da kudirin ta na bada fifiko wajen magance rikice-rikice da kuma dakile cutar da fararen hula a yayin da jami’an ke kokarin kawar da masu data kayar baya.

Kwamandan Kwalejin tsaro ta kasar Rear Admiral Murtala Bashir ne ya bayyana hakan a yayin wani taron karawa juna sani da cibiyar yaki da rikece-rikice (CIVIC) tare da hadin gwuiwar tsofaffen daliban kwalejin tsaron ta kasa (AANDEC) suka shirya a wani bangare na magance cin zarafi da ake zargin jami’an na yiwa fararen hula.

Da yake jawabi daraktan cibiyar ta CIVIC ta kasar Mr Benson Olugbuo ya jaddada cewa kare fararen hula a yanayin tsaro na da matukar muhimmanci saboda yawaitar rikice-rikicen a fadin kasar.

Ya bukaci dakarun tsaro da su ci gaba da gudanar da ayyukansu na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin Al’umma, tare da yin dukkan mai yiwuwa wajen dakile cutar da fararen hula a yayin gudanr da ayyukan wanzan da zaman lafiya.

Olugbuo ya bayyana cewa na daga cikin dalilin daya sa aka gudanar da taron, domin atabbatar da cewa sojoji sun bi ka’idojin aiki a yayin gudanar da ayyukan tsaro.

Shima da yake bayani a yayin bitar Shugaban Tsofaffin daliban kwalejin na kasar Air Commodore Darlington Abdullahi (Mai ritaya) ya bukaci fararen hula da su hada kai da sojoji ta hanayar musayar sahihan bayanai da zai taimaka wajen yakar ‘yan ta’adda masu tada kayar baya.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp