Home Labarai Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kudirin Ta Na Kare Fararen Hular...

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kudirin Ta Na Kare Fararen Hular Kasar

Rundunar sojin Nijeriya ta tabbatar da kudirin ta na bada fifiko wajen magance rikice-rikice da kuma dakile cutar da fararen hula a yayin da jami’an ke kokarin kawar da masu data kayar baya.

Kwamandan Kwalejin tsaro ta kasar Rear Admiral Murtala Bashir ne ya bayyana hakan a yayin wani taron karawa juna sani da cibiyar yaki da rikece-rikice (CIVIC) tare da hadin gwuiwar tsofaffen daliban kwalejin tsaron ta kasa (AANDEC) suka shirya a wani bangare na magance cin zarafi da ake zargin jami’an na yiwa fararen hula.

Da yake jawabi daraktan cibiyar ta CIVIC ta kasar Mr Benson Olugbuo ya jaddada cewa kare fararen hula a yanayin tsaro na da matukar muhimmanci saboda yawaitar rikice-rikicen a fadin kasar.

Ya bukaci dakarun tsaro da su ci gaba da gudanar da ayyukansu na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin Al’umma, tare da yin dukkan mai yiwuwa wajen dakile cutar da fararen hula a yayin gudanr da ayyukan wanzan da zaman lafiya.

Olugbuo ya bayyana cewa na daga cikin dalilin daya sa aka gudanar da taron, domin atabbatar da cewa sojoji sun bi ka’idojin aiki a yayin gudanar da ayyukan tsaro.

Shima da yake bayani a yayin bitar Shugaban Tsofaffin daliban kwalejin na kasar Air Commodore Darlington Abdullahi (Mai ritaya) ya bukaci fararen hula da su hada kai da sojoji ta hanayar musayar sahihan bayanai da zai taimaka wajen yakar ‘yan ta’adda masu tada kayar baya.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp