Home Labarai Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kudirin Ta Na Kare Fararen Hular...

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kudirin Ta Na Kare Fararen Hular Kasar

Rundunar sojin Nijeriya ta tabbatar da kudirin ta na bada fifiko wajen magance rikice-rikice da kuma dakile cutar da fararen hula a yayin da jami’an ke kokarin kawar da masu data kayar baya.

Kwamandan Kwalejin tsaro ta kasar Rear Admiral Murtala Bashir ne ya bayyana hakan a yayin wani taron karawa juna sani da cibiyar yaki da rikece-rikice (CIVIC) tare da hadin gwuiwar tsofaffen daliban kwalejin tsaron ta kasa (AANDEC) suka shirya a wani bangare na magance cin zarafi da ake zargin jami’an na yiwa fararen hula.

Da yake jawabi daraktan cibiyar ta CIVIC ta kasar Mr Benson Olugbuo ya jaddada cewa kare fararen hula a yanayin tsaro na da matukar muhimmanci saboda yawaitar rikice-rikicen a fadin kasar.

Ya bukaci dakarun tsaro da su ci gaba da gudanar da ayyukansu na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin Al’umma, tare da yin dukkan mai yiwuwa wajen dakile cutar da fararen hula a yayin gudanr da ayyukan wanzan da zaman lafiya.

Olugbuo ya bayyana cewa na daga cikin dalilin daya sa aka gudanar da taron, domin atabbatar da cewa sojoji sun bi ka’idojin aiki a yayin gudanar da ayyukan tsaro.

Shima da yake bayani a yayin bitar Shugaban Tsofaffin daliban kwalejin na kasar Air Commodore Darlington Abdullahi (Mai ritaya) ya bukaci fararen hula da su hada kai da sojoji ta hanayar musayar sahihan bayanai da zai taimaka wajen yakar ‘yan ta’adda masu tada kayar baya.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp