Home Labarai Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kudirin Ta Na Kare Fararen Hular...

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kudirin Ta Na Kare Fararen Hular Kasar

Rundunar sojin Nijeriya ta tabbatar da kudirin ta na bada fifiko wajen magance rikice-rikice da kuma dakile cutar da fararen hula a yayin da jami’an ke kokarin kawar da masu data kayar baya.

Kwamandan Kwalejin tsaro ta kasar Rear Admiral Murtala Bashir ne ya bayyana hakan a yayin wani taron karawa juna sani da cibiyar yaki da rikece-rikice (CIVIC) tare da hadin gwuiwar tsofaffen daliban kwalejin tsaron ta kasa (AANDEC) suka shirya a wani bangare na magance cin zarafi da ake zargin jami’an na yiwa fararen hula.

Da yake jawabi daraktan cibiyar ta CIVIC ta kasar Mr Benson Olugbuo ya jaddada cewa kare fararen hula a yanayin tsaro na da matukar muhimmanci saboda yawaitar rikice-rikicen a fadin kasar.

Ya bukaci dakarun tsaro da su ci gaba da gudanar da ayyukansu na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin Al’umma, tare da yin dukkan mai yiwuwa wajen dakile cutar da fararen hula a yayin gudanr da ayyukan wanzan da zaman lafiya.

Olugbuo ya bayyana cewa na daga cikin dalilin daya sa aka gudanar da taron, domin atabbatar da cewa sojoji sun bi ka’idojin aiki a yayin gudanar da ayyukan tsaro.

Shima da yake bayani a yayin bitar Shugaban Tsofaffin daliban kwalejin na kasar Air Commodore Darlington Abdullahi (Mai ritaya) ya bukaci fararen hula da su hada kai da sojoji ta hanayar musayar sahihan bayanai da zai taimaka wajen yakar ‘yan ta’adda masu tada kayar baya.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp