Home Labarai Majalisar Wakilan Nijeriya ta Zargi NNPC Da Badakalar Dala Biliyan 10 Na...

Majalisar Wakilan Nijeriya ta Zargi NNPC Da Badakalar Dala Biliyan 10 Na Tallafin Man Fetur

Majalisar wakilan Nijeriya ta yi zargin cewa an sace sama da Dalar Amurka Biliyan 10 na danyen man fetur, ta hanyar badakalar tallafin Man wanda kamfanin man fetur na kasar NNPC da sauran masu ruwa da tsaki a kamfanin su ka yi.

Don haka majalisar ta kafa wani kwamitin wucin gadi da zai binciki tsarin tallafin man fetur tsakanin shekarar 2017 zuwa 2021 da ga kamfanin na NNPC ya yi.

Hakan ya biyo bayan amincewa da kudirin da Dan majalisa mai wakiltar Edo Sergious Ogun ya shigar gaban majalisar a ranar laraba a birnin tarayya Abuja.

Ta cikin kudirin nasa, Mista Ogun yace an sanar da shi cewa a shekarar 2002, kamfanin na NNPC ya sayi danyen mai a farashin kasuwannin duniya, wanda ya kai ganga 445,000 a ko wacce rana.

Ya kara da cewa anyi hakan ne domin bada damar samar da man da ake amfani da shi a cikin gida, amma abin damuwar shine yadda a shekarar 2002 matatun man Nijeriya ke samar da ganga 445,000 a kowacce rana.

Sai dai kuma yace daga bisani karfin matatun ya ragu zuwa sifili sakamakon rashin inganci da kuma zargin cin hanci da rashawa ga masu ruwa da tsaki ya durkusar da fannin.

By PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp