Home Labarai Majalisar Wakilan Nijeriya ta Zargi NNPC Da Badakalar Dala Biliyan 10 Na...

Majalisar Wakilan Nijeriya ta Zargi NNPC Da Badakalar Dala Biliyan 10 Na Tallafin Man Fetur

Majalisar wakilan Nijeriya ta yi zargin cewa an sace sama da Dalar Amurka Biliyan 10 na danyen man fetur, ta hanyar badakalar tallafin Man wanda kamfanin man fetur na kasar NNPC da sauran masu ruwa da tsaki a kamfanin su ka yi.

Don haka majalisar ta kafa wani kwamitin wucin gadi da zai binciki tsarin tallafin man fetur tsakanin shekarar 2017 zuwa 2021 da ga kamfanin na NNPC ya yi.

Hakan ya biyo bayan amincewa da kudirin da Dan majalisa mai wakiltar Edo Sergious Ogun ya shigar gaban majalisar a ranar laraba a birnin tarayya Abuja.

Ta cikin kudirin nasa, Mista Ogun yace an sanar da shi cewa a shekarar 2002, kamfanin na NNPC ya sayi danyen mai a farashin kasuwannin duniya, wanda ya kai ganga 445,000 a ko wacce rana.

Ya kara da cewa anyi hakan ne domin bada damar samar da man da ake amfani da shi a cikin gida, amma abin damuwar shine yadda a shekarar 2002 matatun man Nijeriya ke samar da ganga 445,000 a kowacce rana.

Sai dai kuma yace daga bisani karfin matatun ya ragu zuwa sifili sakamakon rashin inganci da kuma zargin cin hanci da rashawa ga masu ruwa da tsaki ya durkusar da fannin.

By PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp