Home Labarai Dakarun Sojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Kubutar Da Mutum 6 Tare da...

Dakarun Sojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Kubutar Da Mutum 6 Tare da Hallaka ‘Yan Bindiga a Jihohin Zamfara Da Katsina

Dakarun sojin Nijeriya karkashin rundunar hadarin Daji sun sami nasarar kubutar da wadanda ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane suka yi garkuwa da su a Rafin Bakura dake karamar hukumar Bakura ta jihar Zamfara dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Wannan dai na kunshe ne ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun daraktan yada labaran rundunar Sojin kasar Manjo Janar Benard Onyeuko, sanarwa mai dauke da kwanan watan 30 ga watan Yuni 2022 tace bayan wani kiran gaggawa da suka samu kan ayyukan ‘yan ta’addan a Rafin Dankura, dakarun su suka tasamma ‘yan bindigar dake shirin yin garkuwa da mutanen nan ne suka sami nasarar kubutar da mutum 6 tare da hallaka ‘yan bindigar guda 2.

Oyeuko yace a yayi sumamen dakarun sun sami nasarar kwato bindiga kirar AK47 guda biyu, gurneti hadin gida guda 2, wayoyin hannu guda 2 da kuma zunzurutun kudi kimanin naira Dubu Biyu da Casa’in da Tara (299,000).

Dakarun sojin saman na Operation HADARIN DAJI  a wani farmaki da suka kai ta sama a ranar 22 ga watan yuni, a kauyen kofar Danya dakare karamar hukumar  Bukkuyum ta jihar Zamfara, bayan wani rahoton hari da aka shirya kaiwa kauyen, rundunar ta sami damar zuwa wurin, inda ta hangi ‘yan ta’addan da sama wanda sun haura dari da hamsin (150) a wata maboyar su.

Nan dakarun suka shiga yin artabu da ‘yan ta’addan wanda hakan yayi sanadiyyar tarwatsa sansanin na su, sakamakon hakan sahihan bayanan dake fitowa daga mazauna yankin na kofar Danya sun ce sama da ‘yan bindiga 82 sun sami muggan raunuka inda aka kashe da dama daga cikin su.

Haka a wani harin makamancin wannan da dakarun su kai kauyen mai gra dake karamar hukumar Faskari a jihar katsina, sun sami nasarar halaka ‘yan ta’addan guda biyu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp