Home Labarai Dakarun Sojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Kubutar Da Mutum 6 Tare da...

Dakarun Sojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Kubutar Da Mutum 6 Tare da Hallaka ‘Yan Bindiga a Jihohin Zamfara Da Katsina

Dakarun sojin Nijeriya karkashin rundunar hadarin Daji sun sami nasarar kubutar da wadanda ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane suka yi garkuwa da su a Rafin Bakura dake karamar hukumar Bakura ta jihar Zamfara dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Wannan dai na kunshe ne ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun daraktan yada labaran rundunar Sojin kasar Manjo Janar Benard Onyeuko, sanarwa mai dauke da kwanan watan 30 ga watan Yuni 2022 tace bayan wani kiran gaggawa da suka samu kan ayyukan ‘yan ta’addan a Rafin Dankura, dakarun su suka tasamma ‘yan bindigar dake shirin yin garkuwa da mutanen nan ne suka sami nasarar kubutar da mutum 6 tare da hallaka ‘yan bindigar guda 2.

Oyeuko yace a yayi sumamen dakarun sun sami nasarar kwato bindiga kirar AK47 guda biyu, gurneti hadin gida guda 2, wayoyin hannu guda 2 da kuma zunzurutun kudi kimanin naira Dubu Biyu da Casa’in da Tara (299,000).

Dakarun sojin saman na Operation HADARIN DAJI  a wani farmaki da suka kai ta sama a ranar 22 ga watan yuni, a kauyen kofar Danya dakare karamar hukumar  Bukkuyum ta jihar Zamfara, bayan wani rahoton hari da aka shirya kaiwa kauyen, rundunar ta sami damar zuwa wurin, inda ta hangi ‘yan ta’addan da sama wanda sun haura dari da hamsin (150) a wata maboyar su.

Nan dakarun suka shiga yin artabu da ‘yan ta’addan wanda hakan yayi sanadiyyar tarwatsa sansanin na su, sakamakon hakan sahihan bayanan dake fitowa daga mazauna yankin na kofar Danya sun ce sama da ‘yan bindiga 82 sun sami muggan raunuka inda aka kashe da dama daga cikin su.

Haka a wani harin makamancin wannan da dakarun su kai kauyen mai gra dake karamar hukumar Faskari a jihar katsina, sun sami nasarar halaka ‘yan ta’addan guda biyu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp