Home Labarai Dakarun Sojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Kubutar Da Mutum 6 Tare da...

Dakarun Sojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Kubutar Da Mutum 6 Tare da Hallaka ‘Yan Bindiga a Jihohin Zamfara Da Katsina

Dakarun sojin Nijeriya karkashin rundunar hadarin Daji sun sami nasarar kubutar da wadanda ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane suka yi garkuwa da su a Rafin Bakura dake karamar hukumar Bakura ta jihar Zamfara dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Wannan dai na kunshe ne ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun daraktan yada labaran rundunar Sojin kasar Manjo Janar Benard Onyeuko, sanarwa mai dauke da kwanan watan 30 ga watan Yuni 2022 tace bayan wani kiran gaggawa da suka samu kan ayyukan ‘yan ta’addan a Rafin Dankura, dakarun su suka tasamma ‘yan bindigar dake shirin yin garkuwa da mutanen nan ne suka sami nasarar kubutar da mutum 6 tare da hallaka ‘yan bindigar guda 2.

Oyeuko yace a yayi sumamen dakarun sun sami nasarar kwato bindiga kirar AK47 guda biyu, gurneti hadin gida guda 2, wayoyin hannu guda 2 da kuma zunzurutun kudi kimanin naira Dubu Biyu da Casa’in da Tara (299,000).

Dakarun sojin saman na Operation HADARIN DAJI  a wani farmaki da suka kai ta sama a ranar 22 ga watan yuni, a kauyen kofar Danya dakare karamar hukumar  Bukkuyum ta jihar Zamfara, bayan wani rahoton hari da aka shirya kaiwa kauyen, rundunar ta sami damar zuwa wurin, inda ta hangi ‘yan ta’addan da sama wanda sun haura dari da hamsin (150) a wata maboyar su.

Nan dakarun suka shiga yin artabu da ‘yan ta’addan wanda hakan yayi sanadiyyar tarwatsa sansanin na su, sakamakon hakan sahihan bayanan dake fitowa daga mazauna yankin na kofar Danya sun ce sama da ‘yan bindiga 82 sun sami muggan raunuka inda aka kashe da dama daga cikin su.

Haka a wani harin makamancin wannan da dakarun su kai kauyen mai gra dake karamar hukumar Faskari a jihar katsina, sun sami nasarar halaka ‘yan ta’addan guda biyu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp