Home Labarai Rundunar Sojin Nijeriya Ta Karbi Mayakan ISWAP 4,770 Da suka Mika Wuya...

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Karbi Mayakan ISWAP 4,770 Da suka Mika Wuya a Jihar Borno

Dakarun sojin dake aikin wanzan da zaman lafiya a yankin Arewa Maso Gabashin Nijeriya na Opration HADIN KAI sun sami nasarar halaka ‘yan ta’adda masu tarin yawa, kame wasu gami da kubutar da mutanen da ‘yan ta’addan suka yi garkuwa da su tare da kwato makamai.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran rundunar sojin na kasa Manjo janar Bernard Onyouko ya fitar, wandda tace a kokarin da dakarun sojin Nijeriyar ke yin a ganin sun samar da sahihin zaman lafiya sun kara kaimi wajen gudanar da ayyukan su a garuruwan Buduwa, hanyar Bama zuwa Pulka, kauyen Tuwe, hanyar Kondugazuwa Kawuri, garin Brema dake Damboa Motor Park, Tashangoto, Benishek, Kukaneta dukkan su a jihar Borno.

Sanarwa ta kara da cewa a ranar 17 da 18 ga watan Yuni, 2022 bataliya ta 152 a kauyen Buduwa dake karamar hukumar Bama ta jihar Borno, a wani artabu tsakanin dakarun sojin Nijeriya da mayakan kungiyar boko Haram tsagin ISWAP dakarun sojin sun sami nasarar halaka mayakan Boko haram 7 yayin da kuma suka halaka barayin Shanu 14 suka kuma kwato kekunan hawa 3.

Haka kuma rundunar ta sami nasarar kama wasu dake hada kai da ‘yan boko haram wajen sama musu kayan Aiki, wanda suka hada da Malam Abach Usman a garin Benshek da kuma wani dan ta’adda daya shahara wajen samar da manfetur ga ‘yan ta’adda mai suna Malam Ibrahim Gira.

Ta cikin sanarwar rundunar ta bayyana cewa yanzu haka dai dakarun nata sun sami nasarar hallaka ‘yan Boko haram 11, tare da kame 11, sannan kuma sun kame barayin shannu 14, gami da kwato bindiga kirara AK47 guda 2, kekune 3, bindigu kirar gida guda 2 da kuma Alburusai masu tsayin mita 7.62mm guda 90 da mota kirar Gulf guda 1.

Haka kuma mambobin kungiyar ta boko haram na cigaba da mika wuya tare da ajje makaman su daga 1 zuwa 15 ga watan Yuni rundunar ta sami nasarar karbar mutum 4,770 wanda suka hadar da maza 864 mata 1,415 da kananan yara 2,490.

Daga bisani sanarwa tace dukkan mayakan kungiyar ta ISWAP da iyalan su da suka mika wuya an killace su, haka kuma dukkan wadanda aka kama an mika su ga hukumomin da suka dace.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp