Home Labarai Dakarun Sojin Nijeriya Sun Tarwatsa Maboyar ‘Yan Ta’adda A Jihar Benue

Dakarun Sojin Nijeriya Sun Tarwatsa Maboyar ‘Yan Ta’adda A Jihar Benue

Dakarun sojin Nijeriya karkashin WHIRL STROKE sun sami nasarar kame wata mota mai lambar Abuja KWL 846 XB makare da yankakkun tsaffin karafunan layin dogo akan hanayar Udei zuwa Makurdi lafiya, gami da wasu mutum 7 dake cikin motar.

Wannan na cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran rundunar sojin Nijeriyar ya Manjo Janar Bernar Onyeuko ya fita a wani bangare na bayyana irin na sarorin da rundunar ke samu wajen kawar da ayyukan ‘yan ta’adda a fadin kasar.

Sanarwar tace tuni aka mika motar da mutun 7 dake cikin ta da ake zargin su da aikata laifin ga hukumomin da suka dace domin fadada bincike.

Haka kuma dakarun na WHIRl STROKE sun sami nasarar kama wani mutum mai suna Mista Ardo Manu Abdulrahman wanda take zargi da bada hayar makamai ga ‘yan ta’adda masu garkuwa da mutane da sauran aikata laifuka a jihar Taraba.

A yayin sumamen rundunar ta sami nasarar kwato wayoyin hannu guda 4 da kudi naira Dubu Saba’in da Hudu da dari uku da arba’in (74,340.00), haka kuma a wani sumamen makaman cin wannan a wata maboyar ‘yan ta’addan a Maraba a mazabar Ukyongun Ityuluv na karamar hukumar Ukum dake jihar Benuwai dakarun sun sami nasarar kama wani mutum Mista Ichen Gbaka da matasar Uwargida Saloma Gbaka da suke hada baki da ‘yan ta’addan.

Sanarwa ta kara da cewa a ranar 24 ga watan Yuni 2022 dakarun sun sami nasara kame wasu masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa su hudu (4) a mazabar Igumale dake karamar hukumar Ado ta jihar Benuwai, wanda tuni suka mika su hannun jami’an ‘Yan Sanda.

A ranar 26 ga watan Yuni, 2022 dakarun soji suka gudanar da wani sumame amaboyar ‘yan ta’addan dake  kauyen Mbahuwuhe dake karamar hukumar Katsina-Ala ta jihar ta Benuwai, a yayin sumamen an halaka ‘yan ta’adda uku (3) tare da kubutar da wanda sukayi garkuwa da shi Auya Tisa, yanzu haka yana karbar magani gami da kulawar likitoci, tare da kwato babur din hawa guda daya (1) wayoyin hannu guda biyu (2) kafin kwato kayan sai da dakarun suka fatattaka maboyar ‘yan bindigar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp