Home Labarai Dakarun Sojin Nijeriya Sun Tarwatsa Maboyar ‘Yan Ta’adda A Jihar Benue

Dakarun Sojin Nijeriya Sun Tarwatsa Maboyar ‘Yan Ta’adda A Jihar Benue

Dakarun sojin Nijeriya karkashin WHIRL STROKE sun sami nasarar kame wata mota mai lambar Abuja KWL 846 XB makare da yankakkun tsaffin karafunan layin dogo akan hanayar Udei zuwa Makurdi lafiya, gami da wasu mutum 7 dake cikin motar.

Wannan na cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran rundunar sojin Nijeriyar ya Manjo Janar Bernar Onyeuko ya fita a wani bangare na bayyana irin na sarorin da rundunar ke samu wajen kawar da ayyukan ‘yan ta’adda a fadin kasar.

Sanarwar tace tuni aka mika motar da mutun 7 dake cikin ta da ake zargin su da aikata laifin ga hukumomin da suka dace domin fadada bincike.

Haka kuma dakarun na WHIRl STROKE sun sami nasarar kama wani mutum mai suna Mista Ardo Manu Abdulrahman wanda take zargi da bada hayar makamai ga ‘yan ta’adda masu garkuwa da mutane da sauran aikata laifuka a jihar Taraba.

A yayin sumamen rundunar ta sami nasarar kwato wayoyin hannu guda 4 da kudi naira Dubu Saba’in da Hudu da dari uku da arba’in (74,340.00), haka kuma a wani sumamen makaman cin wannan a wata maboyar ‘yan ta’addan a Maraba a mazabar Ukyongun Ityuluv na karamar hukumar Ukum dake jihar Benuwai dakarun sun sami nasarar kama wani mutum Mista Ichen Gbaka da matasar Uwargida Saloma Gbaka da suke hada baki da ‘yan ta’addan.

Sanarwa ta kara da cewa a ranar 24 ga watan Yuni 2022 dakarun sun sami nasara kame wasu masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa su hudu (4) a mazabar Igumale dake karamar hukumar Ado ta jihar Benuwai, wanda tuni suka mika su hannun jami’an ‘Yan Sanda.

A ranar 26 ga watan Yuni, 2022 dakarun soji suka gudanar da wani sumame amaboyar ‘yan ta’addan dake  kauyen Mbahuwuhe dake karamar hukumar Katsina-Ala ta jihar ta Benuwai, a yayin sumamen an halaka ‘yan ta’adda uku (3) tare da kubutar da wanda sukayi garkuwa da shi Auya Tisa, yanzu haka yana karbar magani gami da kulawar likitoci, tare da kwato babur din hawa guda daya (1) wayoyin hannu guda biyu (2) kafin kwato kayan sai da dakarun suka fatattaka maboyar ‘yan bindigar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp