Home Labarai An bukaci Jami’an yada labaran (PROs) na Hukumar (NCS) Da Suke...

An bukaci Jami’an yada labaran (PROs) na Hukumar (NCS) Da Suke Yin Amfani da Kayan Aikin Yada Labarai Na Zamani

An bukaci Jami’an yada labaran (PROs) na hukumar hana fasa kwauri na Nijeriya (NCS) da suke yin amfani da kayan aikin yada labarai na zamani.

An yi wannan kira ne a yayin wani taron horaswa da hukumar ta shirya wa masu Magana da yawunta.

Da yake Magana a wajen taron horaswa kwamandan dake lora da sashen horas da jami’an Kwastam (CTC) dake Ikeja, Kwantorola Kalamu Ayinde Aremu, ya bayyana cewa yin amfani da sabuwar fasahar zamani zai taimaka matuka wajen sake daga darajar hukumar.

Kakakin hukaumar na kasa DC Timi Bomodi yace, an gadanar da wannan horaswa domin  baiwa jami’an sashin hulda da jama’a na hukumar horon da zai taimaka musu wajen gudanar da ayyukan su yadda ya dace da zamani.

Da yake gabatar da Makala mai take “Effective Public Communication” a yayin taron horaswar Babban mai tace Labarai na jaridar PRNigeria, Yushau Shuaib ya bayyana cewa an sami gagarumin cigaba a fannin sadarwa, ta hanyar sauyi aka samu wajen yin hulda da jama’a.

Sauran wadanda suka gabatar da Makaloli kan matsalaolin da jami’an ke fuskanta, a yayin taron horaswar sun hadar da Dr. Ganiu Okunnu na Jami’ar jihar Legas (LASU) da Abayomi Adisa na BBC, sun bukaci mahalarta taron dasu yi amfani da kayan sadarwa na zamani a yayin da suke gudanar da ayyukan su.

Wanda suka ce yin hakan zai taimaka musu matuka wajen samun kyakkyawar alaka da wadanda suke son sakon ya isa gare su.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp