Home Labarai An bukaci Jami’an yada labaran (PROs) na Hukumar (NCS) Da Suke...

An bukaci Jami’an yada labaran (PROs) na Hukumar (NCS) Da Suke Yin Amfani da Kayan Aikin Yada Labarai Na Zamani

An bukaci Jami’an yada labaran (PROs) na hukumar hana fasa kwauri na Nijeriya (NCS) da suke yin amfani da kayan aikin yada labarai na zamani.

An yi wannan kira ne a yayin wani taron horaswa da hukumar ta shirya wa masu Magana da yawunta.

Da yake Magana a wajen taron horaswa kwamandan dake lora da sashen horas da jami’an Kwastam (CTC) dake Ikeja, Kwantorola Kalamu Ayinde Aremu, ya bayyana cewa yin amfani da sabuwar fasahar zamani zai taimaka matuka wajen sake daga darajar hukumar.

Kakakin hukaumar na kasa DC Timi Bomodi yace, an gadanar da wannan horaswa domin  baiwa jami’an sashin hulda da jama’a na hukumar horon da zai taimaka musu wajen gudanar da ayyukan su yadda ya dace da zamani.

Da yake gabatar da Makala mai take “Effective Public Communication” a yayin taron horaswar Babban mai tace Labarai na jaridar PRNigeria, Yushau Shuaib ya bayyana cewa an sami gagarumin cigaba a fannin sadarwa, ta hanyar sauyi aka samu wajen yin hulda da jama’a.

Sauran wadanda suka gabatar da Makaloli kan matsalaolin da jami’an ke fuskanta, a yayin taron horaswar sun hadar da Dr. Ganiu Okunnu na Jami’ar jihar Legas (LASU) da Abayomi Adisa na BBC, sun bukaci mahalarta taron dasu yi amfani da kayan sadarwa na zamani a yayin da suke gudanar da ayyukan su.

Wanda suka ce yin hakan zai taimaka musu matuka wajen samun kyakkyawar alaka da wadanda suke son sakon ya isa gare su.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp